Aminiya:
2025-06-15@21:30:05 GMT

Tsohon Gwamnan Oyo Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya

Published: 6th, April 2025 GMT

Tsohon Gwamna Jihar Oyo, Omololu Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya.

Wata sanarwa da iyalansa suka fitar ta ce ya rasu yayin da rage kwanaki tara kacal ya cika shekaru 90 a doron ƙasa.

Finafinan Kannywood da suke tashe da kuma manyan marubutansu An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36

Tsohon gwamnan wanda aka haifa a ranar 14 ga watan Afrilun 1935, ya rasu ne da misalin ƙarfe 1:40 na daren ranar 6 ga watan Afrilun 2025.

Bayanai sun ce a bayan nan ya yi ’yar taƙaitacciyar jinya da ke da alaƙa da mutanen da shekarunsu suka ja.

Olunloyo ya riƙe muƙamin Gwamnan Oyo daga ranar 1 ga watan Oktoban 1983 zuwa 31 ga watan Disamban 1983 lokacin da Janar Muhammadu Buhari ya karɓi mulki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Oyo tsohon gwamna

এছাড়াও পড়ুন:

Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka

An samu cece-ku-ce a Jihar Sakkwato bayan da wata jita-jita ta yaɗu cewa Mataimakin Gwamnan jihar, ya karɓi shanu 400 da aka tanadar domin tallafa wa marasa galihu domin yin layya a lokacin Sallah Babba.

An ce shanun wata ƙungiya ce daga ƙasar Turkiyya ta bayar da su, ta hannun Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar, domin tallafa wa waɗanda ba su da halin yin layya.

Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna

Sai dai an zargi Mataimakin Gwamnan da karɓe su don amfanin kansa.

Wannan batu ya jawo jama’a a jihar suk dinga bayyana ra’ayoyinsu, inda wasu ke zargin an fifita jami’an gwamnati fiye da talakawa da aka yi nufin bai qa shanun.

Wasu sun zargi cewa malamai, limamai, ‘yan siyasa da ƙungiyoyin addini ne suka fi cin moriyar shanun.

Sai dai a wata hira da wakilinmu ya yi, da mataimakin gwamnan ya musanta karɓar shanun.

Ya ce: “Hukumar Zakka ce ke raba wa ’yan gudun hijira da ke fama da matsalar tsaro kamar a Sabon Birni da Isa.

“A shekarar da ta gabata sun karɓi shanu 20 kowane. Haka nan Illela da Gwadabawa sun samu goma-goma.”

Ya ƙara da cewa ba shi da hannu kai-tsaye, domin an tuntuɓar shi ne kawai a matsayin wanda zai jagoranci rarraba shanun ga jama’ar yankin da ke ƙarƙashinsa.

Shugaban Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar, Malam Muhammad Lawal Maidoki, ya ƙara bayyana cewa:

“Mataimakin gwamna bai karɓi shanun ba. An kafa kwamiti ƙarƙashinsa domin kula da rabon a yankin Gabas da ke fama da matsalar tsaro. Shanun sun ƙare kafin a gama rabawa. An ware 150, amma 106 ne aka samu.”

Ya kuma bayyana cewa sun yi niyyar yanka shanu 4,500 amma saboda wasu matsaloli, ciki har da rashin samun dabbobi da suka cika sharuɗan layya, sun yanka 3,000 kacal.

Malam Maidoki ya nemi afuwa ga duk wanda bai samu shanun ba, da waɗanda aka saba bai wa amma aka kasa ba su, da waɗanda suke tsammanin samun amma ba su samu ba.

Ya ƙara da cewa sun rubuta sunayen waɗanda ba su samu ba domin tunawa da su a shekara mai zuwa.

“Muna fata Allah Ya kawo mu wata shekara cikin lafiya da dama don ci gaba da tallafa wa marasa ƙarfi a irin wannan lokaci,” in ji shi.

A cewar hukumar, shirin ya laƙume sama da Naira biliyan ɗaya, kuma an raba naman layya ga dubban mutane da ba su samu damar yin yanka ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya