MDD Ta Ware Dala Miliyan 5 Domin Daukar Matakin Da Ya Dace Wajen Tunkarar Ambaliyar Ruwa
Published: 14th, February 2025 GMT
Tawagar ta tattaro hukumomi da suka hada da hukumar kula da yanayi (NiMET), hukumar kula da ayyukan ruwa, da hukumar bada agajin gaggawa ta kasa karkashin kulawar ofishin mataimakin shugaban kasa. Wannan yana tare da hadin gwiwar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da ayyukan jin kai (OCHA).
A duk duniya, OCHA, wacce ke kula da CERF da Asusun Kula da Ruwa na Kasa (CBPFs) irin su Asusun Ba da Agajin Gaggawa (NHF), tana jagorantar matakai don taimaka wa miliyoyin mutane ta hanyar magance annoba kamar ambaliyar ruwa, fari, da kwalara.
A watan Oktoban 2024, CERF ta saki Dala miliyan 5 domin a kara kaimi wajen magance ambaliyar ruwa da kuma magance muhimman bukatu a jihohin Borno da Bauchi a yankin arewa maso gabas da Jihar Sokoto a arewa maso yamma. Kudaden CERF din ya cika dalar Amurka miliyan 6 da hukumar ta NHF ta ware (wanda ya hada da dala miliyan 2 domin daukar matakan da suka dace a dauka tare da yawaitar ambaliyar ruwa da ta raba kimanin mutum 400,000 da muhallansu a Jihar Borno. Ambaliyar ruwa ta lalata abubuwan more rayuwa tare da lalata daruruwan kadada na gonakin noma kafin girbi).
A cewar hasashen yanayi na 2025 da NiMET ta gudanar, ana sa ran fara damina a jihohin Arewa irin su Bauchi, Borno, Jigawa, Kano, Katsina, Sokoto, Yobe da Zamfara, tsakanin farkon watan Yuni da Yulin 2025. Wannan lokacin ya zo daidai da lokacin rani (a tsakanin girbi), lokacin da akafi samun karancin abinci sannan kuma farashin abinci mai gina jiki ke kara tashi. Shirye-shirye a kan lokaci game da wadannan abubuwa na da mahimmanci.
এছাড়াও পড়ুন:
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Ya kuma bukaci da a ci gaba da hada hannu da masu ruwa da tsaki a fannin, musamman domin dakile kalubalen da ake fuskanta na rashin amfana da albarkatun da ke madatsar ruwan, musamman domin kara bunkasa fannin aikin noma da kuma kara samar da wadataccen abinci.
A nasu martanin daban-daban, wasu daga cikin manoman sun yi kira ga hukumar ta HJRBDA, da ta samar musu da Taraktocin noma a daminar bana da kuma lokacin noman rani.
Tawagar ta hukumar HJRBDA, ta ziyarci wuraren adana ruwa; ciki har da na Challawa, Dam din Gorge, wanda ke adana ruwa mai karfin tsawon zurfin mita miliyan 962 da Dam din Tiga, wanda ke iya adana ruwan da zurfinsa ya kai kimanin mita biliyan 1.968 da madatsar ruwan ta Ruwan Kanya da ke iya adana ruwan da ya kai zurfin mita miliyan 50.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp