MDD Ta Ware Dala Miliyan 5 Domin Daukar Matakin Da Ya Dace Wajen Tunkarar Ambaliyar Ruwa
Published: 14th, February 2025 GMT
Tawagar ta tattaro hukumomi da suka hada da hukumar kula da yanayi (NiMET), hukumar kula da ayyukan ruwa, da hukumar bada agajin gaggawa ta kasa karkashin kulawar ofishin mataimakin shugaban kasa. Wannan yana tare da hadin gwiwar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da ayyukan jin kai (OCHA).
A duk duniya, OCHA, wacce ke kula da CERF da Asusun Kula da Ruwa na Kasa (CBPFs) irin su Asusun Ba da Agajin Gaggawa (NHF), tana jagorantar matakai don taimaka wa miliyoyin mutane ta hanyar magance annoba kamar ambaliyar ruwa, fari, da kwalara.
A watan Oktoban 2024, CERF ta saki Dala miliyan 5 domin a kara kaimi wajen magance ambaliyar ruwa da kuma magance muhimman bukatu a jihohin Borno da Bauchi a yankin arewa maso gabas da Jihar Sokoto a arewa maso yamma. Kudaden CERF din ya cika dalar Amurka miliyan 6 da hukumar ta NHF ta ware (wanda ya hada da dala miliyan 2 domin daukar matakan da suka dace a dauka tare da yawaitar ambaliyar ruwa da ta raba kimanin mutum 400,000 da muhallansu a Jihar Borno. Ambaliyar ruwa ta lalata abubuwan more rayuwa tare da lalata daruruwan kadada na gonakin noma kafin girbi).
A cewar hasashen yanayi na 2025 da NiMET ta gudanar, ana sa ran fara damina a jihohin Arewa irin su Bauchi, Borno, Jigawa, Kano, Katsina, Sokoto, Yobe da Zamfara, tsakanin farkon watan Yuni da Yulin 2025. Wannan lokacin ya zo daidai da lokacin rani (a tsakanin girbi), lokacin da akafi samun karancin abinci sannan kuma farashin abinci mai gina jiki ke kara tashi. Shirye-shirye a kan lokaci game da wadannan abubuwa na da mahimmanci.
এছাড়াও পড়ুন:
Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.
Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.
Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr. Bello Jamoh, za su gudanar da cikakken binciken lafiyar maniyata kafin tafiyar su zuwa kasa mai tsarki da zai gudana a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna.
Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).
Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.
“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.
Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.
“Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.
Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.
Adamu Yusuf