Jagora: Idan Amurka Ta Yi Barazana Ga Tsaron Iran Zata Fuskanci Mayar Da Martani
Published: 8th, February 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Idan Amurka ta yi barazana ga tsaron kasar Iran, to lallai Iran ta kalubalance ta
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Tattaunawa da Amurka ba wayo ba ce, kuma ba hikima ba ce, kuma gogewa ta tabbatar da hakan.
Yayin ganawarsa da tawagar kwamandojin sojojin sama da na sararin samaniya na sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya jaddada cewa: Idan Amurkawa suka yi barazana wa Iran, to lallai za su fuskanci mayar da martani, idan kuma suka aiwatar da wannan barazanar, to za su fuskanci mayar da martani Iran mai gauni, kamar yadda idan suka kawo hari kan kasar Iran, za su fuskanci mayar da martani kan harkokin da suka shafi tsaronsu ba tare da wata shakka ba.
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya kara da cewa: Zaman tattauna da gwamnati irin Amurka aiki ne na rashin hankali da rashin hankali da babu hikima ciki.
Jagoran ya kara da cewa: A cikin shekaru goma da suka gabata, Iran ta zauna kan teburin tattaunawa da Amurka, kuma aka kulla yarjejeniya a tsakaninsu, amma wanda ke jagorancin Amurka a yau, shi ne ya rusa wannan yarjejeniyar. Kuma a gabanin haka lamarin ya kasance, waɗanda mutane ba su mutunta duk wata yarjejeniyar da aka kulla da su, kuma manufar cimma yarjejeniyar ita ce dage takunkumi kan Iran, amma ba su dage shi ba!
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Jagoran juyin juya halin
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya zargi Isra’ila da yin zagon kasa ga diflomasiyya ta hanyar tsallaka jajayen layukan kasar Iran, da kuma ta’azzara rikici da kasashen yammacin duniya, yana mai bayyana cewa, ba za a iya yin shawarwari a halin da ake ciki ba.
Sanarwar dai na nuni da koma baya sosai a yunkurin diflomasiyya na Iran da kasashen Yamma, musamman yadda tashe-tashen hankula ke kara ta’azzara bayan matakin sojin Isra’ila.
Matakin na Isra’ila da hadin kai tare da Amurka na a matsayin kokari na kawar da duk wata dama ta cimma sakamakon shawarwari.
“Ba za a iya shawarwarin ba yayin da a lokaci guda ake barin gwamnatin kisan kare dangi ta kai hari kan Iran.”
“Ba Isra’ila za ta aikata irin wadannan laifuka ba tare da amincewar Amurka ba.”
Iran dai na kallon hare-haren da Isra’ila ta kai a baya-bayan nan a matsayin wani hari kai tsaye ga ‘yan kasarta.