HausaTv:
2025-05-01@04:08:59 GMT

Jagora: Idan Amurka Ta Yi Barazana Ga Tsaron Iran Zata Fuskanci Mayar Da Martani

Published: 8th, February 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Idan Amurka ta yi barazana ga tsaron kasar Iran, to lallai Iran ta kalubalance ta

Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Tattaunawa da Amurka ba wayo ba ce, kuma ba hikima ba ce, kuma gogewa ta tabbatar da hakan.

Yayin ganawarsa da tawagar kwamandojin sojojin sama da na sararin samaniya na sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya jaddada cewa: Idan Amurkawa suka yi barazana wa Iran, to lallai za su fuskanci mayar da martani, idan kuma suka aiwatar da wannan barazanar, to za su fuskanci mayar da martani Iran mai gauni, kamar yadda idan suka kawo hari kan kasar Iran, za su fuskanci mayar da martani kan harkokin da suka shafi tsaronsu ba tare da wata shakka ba.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya kara da cewa: Zaman tattauna da gwamnati irin Amurka aiki ne na rashin hankali da rashin hankali da babu hikima ciki.

Jagoran ya kara da cewa: A cikin shekaru goma da suka gabata, Iran ta zauna kan teburin tattaunawa da Amurka, kuma aka kulla yarjejeniya a tsakaninsu, amma wanda ke jagorancin Amurka a yau, shi ne ya rusa wannan yarjejeniyar. Kuma a gabanin haka lamarin ya kasance, waɗanda mutane ba su mutunta duk wata yarjejeniyar da aka kulla da su, kuma manufar cimma yarjejeniyar ita ce dage takunkumi kan Iran, amma ba su dage shi ba!

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jagoran juyin juya halin

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72

Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Bangaren Guda kuma na sa’o’ii 72 ko kwanaki 3, daga 8-10 na watan Mayu mai zuwa.

Jaridar Daily Trust ta Najeriya nakalto jakadan kasar Rasha a Abuja yana fadar haka a wani taro baje kolin hotinan yaki Rasah da Nazi a dai dai lokacinda kasar take cikar shekaru 80 da samun nasara a kan sojojin Nazi a karshen yakin duniya na II a Abuja.

Andrey Podelyshev yace idan kasar Ukraine ta zami da tsagaita wuta a cikin wadannan kwanaki ba laifi, amma kuma idan sojojinta sun kai wani hari a kan rasha ta zata rama da hare-hare masu tsanani.

Shugaban Volodimir Zelesky dai tuni ya yi watsi da tsagaita wutar ya kura kara da cewa Rasha tana son ta ja hankalin duniya ne da wannan tsagaita wuta, don amfanin kanta a yakin da suke fafatawa. A halin yanzu dai an dai kwanaki kimani 1,159 aka fafatawa tsakanin kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba