Kasar Iran Ta Ce; Amurka Tana Kalubalantar Cibiyoyin Kasa Da Kasa Saboda Jiji Da Kanta
Published: 8th, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana cewa: Amurka tana kalubalantar cibiyoyin kasashen Duniya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Dabi’ar Amurka ta aiwatar da dokokin cikin gida ta ketara kan iyakokinta, inda a yanzu take tunkarar cibiyoyin kasa da kasa.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya rubuta a shafin dandalin “X” dangane da sakamakon takunkumin da Amurka ta kakabawa cibiyoyin kasa da kasa misalin kotun hukunta manyan laifuka ta duniya a matsayin tarayya a tafka laifuka da gwamnatin mamayar Isra’ila, yana mai jaddada cewa: Amurka ta ketara haddinta na aiwatar da dokokin a cikin gidan kasarta, ta ketara kan iyakokinta yanzu kan cibiyoyin kasa da kasa.
Baqa’i ya kara da cewa: Kakaba takunkumi kan kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa domin gudanar da bincike kan munanan laifukan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, wani abu ne da ba a taba ganin irinsa ba a tsawon tarihin Amurka na hada baki da wani gungun ‘yan mamaya masu nuna wariyar al’umma wadanda suke aikata muggan laifuka iri-iri ciki har da aiwatar da kisan kare dangi kan al’ummar Falastinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a yi koyi daga akidun dan mazan jiya, kuma jagora na gari Chen Yun, tare da kara azamar dorar da kyawawan dabi’unsa cikin himma da kwazo, don gina kasar Sin mai matukar karfi.
Shugaba Xi, wanda shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar koli ta rundunar sojojin kasar, ya yi kiran ne a yau Juma’a, cikin jawabin da ya gabatar, yayin taron bikin murnar cika shekaru 120 da haihuwar Chen Yun, taron da ya gudana a babban dakin taruwar jama’a dake tsakiyar birnin Beijing
Shugaban na Sin ya ce, an haifi Chen a shekarar 1905, ya kuma shiga JKS a shekarar 1925. Ya kuma kasance shahararren dan gwagwarmaya a rundunar ‘yantar da al’umma kuma dattijon arziki, kana daya daga cikin kusoshin da suka kafa tsarin tattalin arziki na gurguzu na kasar Sin. Kazalika, ya kasance muhimmin memba cikin jerin shugabannin JKS zangon farko mai Mao Zedong a matsayin babban jigo, kana da shugabannin JKS zango na biyu mai Deng Xiaoping a matsayin babban jigo. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp