Aminiya:
2025-09-17@22:08:07 GMT

An kashe ɗan banga da yin garkuwa da ’yan mata 6 a Neja

Published: 7th, February 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da wasu ’yan mata shida masu shekaru tsakanin 15 zuwa 17 a yankin unguwar Pandogari da ke Ƙaramar hukumar Rafi ta Jihar Neja.

Mazauna garin sun shaida wa Aminiya cewa, da tsakar daren Laraba ne ’yan bindigar suka kaiwa unguwarsu hari inda suka kashe wani ɗan banga mai suna Aliyu Aminu tare da yin garkuwa da ’yan matan.

’Yan fashin teku sun sace jirgin fasinja mutum 11 sun ɓace a Ribas Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace

Mazauna yankin sun ce, maharan da suke da yawa sun shiga cikin unguwar ne daga yankin Birnin Gwari, ta Kwalejin fasaha ta Mamman Kontagora da ke Pandogari.

Majiyoyi sun ce an kai ’yan matan da aka sace zuwa dajin Kwangel.

Ɗaya daga cikin majiyar ta ce, ’yan bindigar sun shiga gida gida a lokacin da suka kai farmakin cikin dare.

“Harin da aka kai a daren Laraba shi ne na uku a cikin mako guda. Tun bayan sasantawa da gwamnatin Jihar Kaduna ta yi da su, sun yi ta kai mana hari. Tattaunawa da sasantawa da mazauna Birnin Gwari ba su amfanar da mu ba.

“Waɗannan hare-haren sun sake dawowa tun ranar da Jihar Kaduna ta sasanta da su a Birnin Gwari. A makon da ya gabata, sun zo sun yi garkuwa da mutane ciki har da mai unguwar. Sun zo sau biyu kafin daren Larabar,” in ji shi.

Shugaban Ƙaramar hukumar Rafi, Ayuba Usman Katako ya tabbatar da faruwar harin a cikin wani shirin Hausa mai suna Tsalle Ɗaya ta gidan rediyon Prestige FM, inda ya ce akwai buƙatar gwamnatocin Neja da Kaduna su haɗa kai don ganin an samu zaman lafiya a jihohin biyu.

“Gaskiya ne ’yan bindiga sun kai hari a unguwar Pandogari. Hasali ma, ba wannan ne kawai harin da aka kai a makonni biyun da suka gabata ba. Harin na Laraba shi ne na uku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dajin Kwangel Rafi

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

 

Ya ce, masu garkuwa da mutanen sun afka gidansa ne a daren Lahadi a lokacin da mazauna gidan ke shirin kwanciya barci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara