Kaduna: Gwamna Uba Sani Ya Tsabtace Harkokin Hajji – NUJ
Published: 8th, February 2025 GMT
An yabawa Gwamna Uba Sani saboda tsabtace harkokin hajji da kuma naɗa kwararru don jagorantar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna.
Shugaban Kungiyar Yan Jaridu ta Kasa reshen Jihar Kaduna, Alhaji AbdulGafaar Alabelewe, ne yayi yabo yayin da jami’an kungiyar suka kai ziyarar ban girma ga hukumar.
NUJ ta kuma bayyana naɗin Malam Salihu S. Abubakar a matsayin Shugaban Hukumar a matsayin wanda ya dace da mukami, inda suka jaddada cewa gaskiyarsa da bin doka da na da matukar muhimmanci wajen ci gaban hukumar.
Alhaji AbdulGafaar ya ce hukumar ta samu nasarori masu yawa a lokacin hajjin da ya gabata, ciki har da maidawa kowane mahajjaci dala 50 daga kudin hadaya da suka biya a Najeriya.
Ya kuma ce mahajjatan jihar Kaduna sun sami matsuguni kusa da Masallacin Harami a Makka, kuma farashinsa ya kasance kasa da wanda Hukumar Kula da Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tsara.
A cewarsa, maidawa mahajjatan shekarar 2023 naira 61,080 cikin gaggawa ya nuna cewa Malam Salihu da kwamitinsa suna da kwazo da himma wajen gyara harkokin hajji.
Alabelewe ya kuma yaba da gyaran da hukumar ta yi wa sansanin mahajjata na Mando, yana mai danganta nasarorin da gaskiya da rikon amana na shugabancin hukumar.
Shugaban NUJ ya sha alwashin ci gaba da hada hannu da hukumar wajen wayar da kan maniyyata, tare da kira ga ‘yan jaridu da su bai wa hukumar cikakken hadin kai.
Da yake mayar da martani, Malam Salihu ya gode wa ‘yan jaridu bisa kyakkyawar dangantaka da hukumar, tare da alkawarin ƙarfafa hulda da su. Ya bukaci su dinga tantance labarai masu shakku kafin wallafawa, yana mai cewa, “kofarmu a bude take don karin bayani.”
Shugaban hukumar ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa goyon bayansa, yana mai cewa duk nasarorin da aka samu saboda tallafinsa ne.
Rel/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Harkokin Kaduna Gwamna Uba
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
Wani magidanci, Malam Jibrin Rabi’u, ya bayyana yadda matarsa, Khadijat Ado, ta ɓace a gidansu da ke unguwar Life Camp a Abuja a ranar Alhamis da ta gabata, sannan kuma aka gano ta a Sakkwato washegari.
Ya shaida wa wakilinmu da yammacin Lahadi, cewa ya dawo gida a ranar Alhamis, sai ya tarar da matarsa ba ta nan.
Malam Jibril ya ce, ya kira wani abokinsa ɗan sanda, wanda ya sanar da ofishin ’yan sanda na Life Camp, Gwarinpa da sauran sassan yankin bayan bincike na farko ya gagara gano inda take.
A cewarsa, na’urar CCTV da ke gidansu ta nuna yadda matarsa ta fita daga gidan cikin natsuwa, har sai da ta fita daga inda kyamarar ke iya ɗauka.
Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a YobeMalam Jibrin ya ce duk da ƙoƙarin da suka yi na gano ta a ranar Alhamis ɗin, ba su samu nasara ba.
Sai dai ya ce da yammacin Juma’a aka kira shi aka shaida masa cewa an gano matarsa a Sakkwato, amma ba ta iya magana.
Ya ce, “Yanzu ma har yanzu ba ta iya magana ba, amma ta dawo cikin hayyacinta. Muna tattaunawa ta hanyar rubutu ne kawai.”
Ya bayyana cewa matarsa ta rubuto masa cewa a ranar da ta ɓace, ta ji kamar wani ana kiranta ne, sai ta buɗe ƙofa ta fita — daga nan kuma ba ta san abin da ya faru ba, sai da ta tsinci kanta a Sakkwato.
A cewar Malam Jibrin, “Ta ce da ta isa Sakkwato, ta haɗu da wata mace wadda ta roƙi takarda da biro, sannan ta rubuta mata abin da ya faru domin ba ta iya magana.”
Ya ce daga nan ne wannan matar ta kira shi, inda ya nemi ta da ta kai matarsa wurin danginsa da ke Sakkwato.
Malam Jibrin ya ce har yanzu matarsa tana Sakkwato, kuma ba ta samu damar yin magana ba, amma ya shirya tafiya Sakkwato yau domin ya dawo da ita gida.
Wata majiyar ’yan sanda a Life Camp ya tabbatar da cewa an kawo rahoton ɓacewar a ranar Alhamis, amma ya ce duk wani ƙarin bayani sai an tuntuɓi hedikwatar rundunar.
An kuma bayyana cewa kiraye-kirayen da aka yi wa jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sanda ta Abuja, DSP Josephine Adeh, ba ta ɗaga wayarta ba.