Kaduna: Gwamna Uba Sani Ya Tsabtace Harkokin Hajji – NUJ
Published: 8th, February 2025 GMT
An yabawa Gwamna Uba Sani saboda tsabtace harkokin hajji da kuma naɗa kwararru don jagorantar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna.
Shugaban Kungiyar Yan Jaridu ta Kasa reshen Jihar Kaduna, Alhaji AbdulGafaar Alabelewe, ne yayi yabo yayin da jami’an kungiyar suka kai ziyarar ban girma ga hukumar.
NUJ ta kuma bayyana naɗin Malam Salihu S. Abubakar a matsayin Shugaban Hukumar a matsayin wanda ya dace da mukami, inda suka jaddada cewa gaskiyarsa da bin doka da na da matukar muhimmanci wajen ci gaban hukumar.
Alhaji AbdulGafaar ya ce hukumar ta samu nasarori masu yawa a lokacin hajjin da ya gabata, ciki har da maidawa kowane mahajjaci dala 50 daga kudin hadaya da suka biya a Najeriya.
Ya kuma ce mahajjatan jihar Kaduna sun sami matsuguni kusa da Masallacin Harami a Makka, kuma farashinsa ya kasance kasa da wanda Hukumar Kula da Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tsara.
A cewarsa, maidawa mahajjatan shekarar 2023 naira 61,080 cikin gaggawa ya nuna cewa Malam Salihu da kwamitinsa suna da kwazo da himma wajen gyara harkokin hajji.
Alabelewe ya kuma yaba da gyaran da hukumar ta yi wa sansanin mahajjata na Mando, yana mai danganta nasarorin da gaskiya da rikon amana na shugabancin hukumar.
Shugaban NUJ ya sha alwashin ci gaba da hada hannu da hukumar wajen wayar da kan maniyyata, tare da kira ga ‘yan jaridu da su bai wa hukumar cikakken hadin kai.
Da yake mayar da martani, Malam Salihu ya gode wa ‘yan jaridu bisa kyakkyawar dangantaka da hukumar, tare da alkawarin ƙarfafa hulda da su. Ya bukaci su dinga tantance labarai masu shakku kafin wallafawa, yana mai cewa, “kofarmu a bude take don karin bayani.”
Shugaban hukumar ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa goyon bayansa, yana mai cewa duk nasarorin da aka samu saboda tallafinsa ne.
Rel/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Harkokin Kaduna Gwamna Uba
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.
Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.
Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.
Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.
“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.
Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.
Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.
“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.