Kaduna: Gwamna Uba Sani Ya Tsabtace Harkokin Hajji – NUJ
Published: 8th, February 2025 GMT
An yabawa Gwamna Uba Sani saboda tsabtace harkokin hajji da kuma naɗa kwararru don jagorantar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna.
Shugaban Kungiyar Yan Jaridu ta Kasa reshen Jihar Kaduna, Alhaji AbdulGafaar Alabelewe, ne yayi yabo yayin da jami’an kungiyar suka kai ziyarar ban girma ga hukumar.
NUJ ta kuma bayyana naɗin Malam Salihu S. Abubakar a matsayin Shugaban Hukumar a matsayin wanda ya dace da mukami, inda suka jaddada cewa gaskiyarsa da bin doka da na da matukar muhimmanci wajen ci gaban hukumar.
Alhaji AbdulGafaar ya ce hukumar ta samu nasarori masu yawa a lokacin hajjin da ya gabata, ciki har da maidawa kowane mahajjaci dala 50 daga kudin hadaya da suka biya a Najeriya.
Ya kuma ce mahajjatan jihar Kaduna sun sami matsuguni kusa da Masallacin Harami a Makka, kuma farashinsa ya kasance kasa da wanda Hukumar Kula da Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tsara.
A cewarsa, maidawa mahajjatan shekarar 2023 naira 61,080 cikin gaggawa ya nuna cewa Malam Salihu da kwamitinsa suna da kwazo da himma wajen gyara harkokin hajji.
Alabelewe ya kuma yaba da gyaran da hukumar ta yi wa sansanin mahajjata na Mando, yana mai danganta nasarorin da gaskiya da rikon amana na shugabancin hukumar.
Shugaban NUJ ya sha alwashin ci gaba da hada hannu da hukumar wajen wayar da kan maniyyata, tare da kira ga ‘yan jaridu da su bai wa hukumar cikakken hadin kai.
Da yake mayar da martani, Malam Salihu ya gode wa ‘yan jaridu bisa kyakkyawar dangantaka da hukumar, tare da alkawarin ƙarfafa hulda da su. Ya bukaci su dinga tantance labarai masu shakku kafin wallafawa, yana mai cewa, “kofarmu a bude take don karin bayani.”
Shugaban hukumar ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa goyon bayansa, yana mai cewa duk nasarorin da aka samu saboda tallafinsa ne.
Rel/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Harkokin Kaduna Gwamna Uba
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
Ya umurci jami’an tsaro su gaggauta kai dauki ba tare da bata lokaci ba don tabbatar da an gurfanar da masu laifin a gaban kuliya, yana mai jaddada cewa za a hukunta duk wanda aka samu dauke da muggan makamai ko kuma aka samu yana da hannu wajen aikata laifuka.
“Ga iyalai da ‘yan uwa da masoyan marigayi Ahmed, ina mika sakon ta’aziyyata, da na gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, kuma muna jimami tare da ku, ina ba ku tabbacin za a yi adalci.
“Ina kuma kira ga jami’an tsaro su kara kaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma sintiri kan tituna, musamman a wuraren da ke fuskantar irin wadannan laifuka. Jama’armu sun cancanci tafiya cikin walwala ba tare da tsoro ko barazana ga rayuka da dukiyoyinsu ba.
“Muna ci gaba da jajircewa wajen kare kowane rai da kuma tabbatar da cewa zaman lafiya da tsaro sun ci gaba da wanzuwa a wannar jiharmu.”
Ya yi kira ga al’umma su tallafa wa jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai masu muhimmanci kan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp