“Yar Sakon Amurka A Kasar Lebanon Morgan Ortagus Tana Shan Mayar Da Martani Daga Bangarori Mabanbanta
Published: 7th, February 2025 GMT
Bangarori mabanbanta na kasar Lebanon suna mayarwa da ‘yar sakon Amurka martani saboda tsoma baki da ta yi a kan yadda za a kafa gwamnati a kasar.
Morgan Ortagus wacce ta gana da jami’an kasar Lebanon ta bayyana cewa, bai kamata a kafa gwamnati a kasar ta wakilan kungiyar Hizbullah a ciki ba.
Kungiyar malaman addinin musulunci ta fitar da bayani da a ciki ta ce; “Furucin mataimakin manzon Amurka a gabas ta tsakiya, Morgan Ortagus wacce ‘yar sahayoniya ce,tsoma baki ne a harkokin cikin gidan Lebanon wanda ya tsallake ka’idojin aikin diplomasiyya.
Ita ma gwamnatin kasar ta Lebanon ta fitar da bayani tana mai cewa abinda Ortugas din ta furta, ra’ayinta ne, bai shafi gwamnatin Lebanon ba.
Shi kuwa shugaban kungiyar ‘yan majalisar dokokin Lebanon masu wakiltar Hizbullah, Muhammad Ra’ad ya bayyana furucin na ‘yar sakon Amurkan da cewa; Hikidi ne da kuma tsoma baki a harkokin cikin gidan Lebanon.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar
Kamfanin dillancin labarun ” Mehr” ya bayyana cewa; Ziyarar da shugaban kasar ta Iran zai kai zuwa Pakistan amsa karan Fira minister Shahbaz Sharif ne.
Bugu da kari ziyarar za a yi ta ne a daidai lokacin da wannan yankin yake fama da sauye-sauye, haka nan kuma za ta mayar da hankali wajen bunkasa alakar kasashen biyu.
Majiyar kasashen biyu, Iran da Pakistan sun ce shugaban kasar ta Iran Mas’ud Fizishkiyan zai fara ziyarar tashi daga birnin Lahor ne, inda zai ziyarci hubbaren shahararren masanin kasar Allamha Muhammad Iqbal, sannan ya nufi binrin Islamaabab domin ganawa da jmai’an gwamnatin kasar.Daga cikin wadanda zai gana da su a can babban birnin kasar da akwai ‘yan siyasa da kuma jami’an soja da su ka hada da shugaban kasa Ali Zardari da Fira minister Shahbaz Sharif.
Bugu da kari shugaban kasar ta Iran zai gana da masanan kasar ta Pakistan da kuma ‘yan kasuwa domin bunkasa alakar tattalinn arziki da alakar al’adu da addini a tsakanin kasashen biyu.
Ta fuskar kasuwancin kuwa,kasashen biyu suna son ganin an kara yawan musayar haja a tsakaninsu domin ta haura dala biliyan 3.
Wannan dai ita ce Ziyara ta biyu da shugaban kasar Iran zai kai kasar Pakistan a cikin shekaru biyu. A cikin watan Aprilu 2024, shugaban kasar Iran shahida Ibrahim Ra’isi ya ziyarci Pakistan.
Watanni biyu da su ka gabata Fira Ministan kasar ta Pakistan Shahbaz Sharif ya kawo Ziyara Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka July 31, 2025 Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu July 31, 2025 Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara July 31, 2025 Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD July 31, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI July 31, 2025 Sojojin Mamaya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza July 31, 2025 Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki July 31, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci