Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah wadai da harin da aka kai kan fararen hula a Sudan

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi Allah wadai da kisan fararen hula a hare-haren da ake kai wa kan asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan tare da jaddada wajibcin mutunta ka’idoji da dokokin kare hakkin bil’adama a kasar.

Baqa’i” ya yi Allah wadai da kisan mutane a hare-haren da ake kai wa kan fararen hula da ababen more rayuwa, musamman asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya bayyana juyayinsa ga wadanda harin baya-bayan nan ya rutsa da su, musamman a birnin El Fasher fadar mulkin Darfur ta Arewa, inda ya jaddada bukatar kiyaye ka’idoji da na dokokin jin kai na kasa da kasa, musamman ka’idar haramta kai hare-hare kan wuraren fararen hula, tare da yin kira da a kawo karshen tashe-tashen hankula da samar da hanyoyin warware rikicin da ke faruwa a Sudan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: fararen hula

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.

Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.

Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.

Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.

Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.

Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran