Iran Ta Yi Watsi Da Shirin Trump Na Tilastawa ‘Yan Gaza Barin Yankinsu
Published: 29th, January 2025 GMT
Iran ta mayar da martani game da shirin shugaban kasar Amurka Donald Trump na tilastawa Falasdinawan Gaza komawa kasashen Jordan da kuma Masar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya yi watsi da shirin na Trump a wani sako a kan shafinsa na X.
Baghaei ya ce, kisan kiyashin da gwamnatin Isra’ila ta kwashe watanni 15 tana yi, ya kasa kawar da Falasdinawa daga tushensu, don haka ba wani abunda zai iya tilasta musu ficewa daga yankinsu.
“Wannan ita ce kasarsu ta asali kuma sun sadaukar da komi don su ci gaba da zama a can kuma su ci gaba da gwagwarmayar neman yancin kai,” a cewar kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran.
Wannan kiran na Trump dai ya zo ne duk da tsananin adawar da Alkahira da Amman suka bayyana wa shirin da ya bayyana da na tsaftace yankin Gaza.
Shi dai Trump ya yi ikirarin cewa matakin na iya “kawo zaman lafiya” a yammacin Asiya idan Masar, Jordan, da sauran kasashen Larabawa suka karbi ‘yan gudun hijirar Falasdinu.
Trump ya ce tuni ya tattauna da Sarki Abdallah na biyu na Jordon kan yiwuwar gina gidaje da kuma kwashe Falasdinawa sama da miliyan daya daga Gaza.
Alkahira da Amman sun yi watsi da shawarar Trump a hukumance.
Manazarta sun ce duk wani shiri na tsugunar da Falasdinawan da suka rasa matsugunnai, zai bai wa gwamnatin Isra’ila uzurin da ta ke bukata na korar al’ummar Gaza da karfi, da kuma sake mamaye yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Kano ta samu nasarar kama mutane 15 da ake zargi da laifuka daban-daban, ciki har da wani kasurgumin dan fashi da makami mai suna Mu’azu Barga, a wani samame da aka lakaba wa suna “Operation Kukan Kura”.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano.
Ya ce samamen, wanda dakaru na musamman suka gudanar a unguwannin Sheka, Ja’oji, da Kurna a ranar 26 ga Yulin 2025, na da nufin gano da kuma hana aikata laifuka, bisa umarnin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun.
Kiyawa ya bayyana cewa, wadanda aka kama ‘yan tsakanin shekaru 14 ne zuwa 28, kuma an same su da wayoyin salula guda hudu da suka sace daga hannun mutane daban-daban.
“Wadanda ake zargin sun amsa laifin aikata sata da fashi, musamman satar wayoyin salula,” In ji shi.
“Mu’azu Barga, wanda ake zargi da kasancewa barawo a lokuta da dama, yana daga cikin wadanda aka kama. Ana danganta shi da laifukan fashi da makami, da kuma. jagorantar hare-hare masu tayar da hankali da fada tsakanin kungiyoyin daba a cikin birnin Kano.”
Kiyawa ya kara da cewa, Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ayyana yaki da duk wani nau’in laifi na daba, tare da jaddada kudurin rundunar na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar.
Ya bayyana godiyar rundunar bisa goyon bayan jama’a, tare da yin kira da su ci gaba da bayar da rahoton duk wani motsi ko mutum da suke zargi da aikata laifi, a ofishin ‘yan sanda mafi kusa.
Abdullahi Jalaluddeen