HausaTv:
2025-09-18@02:16:59 GMT

Iran Ta Yi Watsi Da Shirin Trump Na Tilastawa ‘Yan Gaza Barin Yankinsu

Published: 29th, January 2025 GMT

Iran ta mayar da martani game da shirin shugaban kasar Amurka Donald Trump na tilastawa Falasdinawan Gaza komawa kasashen Jordan da kuma Masar.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya yi watsi da shirin na Trump a wani sako a kan shafinsa na X.

Baghaei ya ce, kisan kiyashin da gwamnatin Isra’ila ta kwashe watanni 15 tana yi, ya kasa kawar da Falasdinawa daga tushensu, don haka ba wani abunda zai iya tilasta musu ficewa daga yankinsu.

“Wannan ita ce kasarsu ta asali kuma sun sadaukar da komi don su ci gaba da zama a can kuma su ci gaba da gwagwarmayar neman yancin kai,” a cewar kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran.    

Wannan kiran na Trump dai ya zo ne duk da tsananin adawar da Alkahira da Amman suka bayyana wa shirin da ya bayyana da na tsaftace yankin Gaza.

Shi dai Trump ya yi ikirarin cewa matakin na iya “kawo zaman lafiya” a yammacin Asiya idan Masar, Jordan, da sauran kasashen Larabawa suka karbi ‘yan gudun hijirar Falasdinu.

Trump ya ce tuni ya tattauna da Sarki Abdallah na biyu na Jordon kan yiwuwar gina gidaje da kuma kwashe Falasdinawa sama da miliyan daya daga Gaza.

Alkahira da Amman sun yi watsi da shawarar Trump a hukumance.

Manazarta sun ce duk wani shiri na tsugunar da Falasdinawan da suka rasa matsugunnai, zai bai wa gwamnatin Isra’ila uzurin da ta ke bukata na korar al’ummar Gaza da karfi, da kuma sake mamaye yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa