HausaTv:
2025-11-02@20:15:45 GMT

Iran Ta Yi Watsi Da Shirin Trump Na Tilastawa ‘Yan Gaza Barin Yankinsu

Published: 29th, January 2025 GMT

Iran ta mayar da martani game da shirin shugaban kasar Amurka Donald Trump na tilastawa Falasdinawan Gaza komawa kasashen Jordan da kuma Masar.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya yi watsi da shirin na Trump a wani sako a kan shafinsa na X.

Baghaei ya ce, kisan kiyashin da gwamnatin Isra’ila ta kwashe watanni 15 tana yi, ya kasa kawar da Falasdinawa daga tushensu, don haka ba wani abunda zai iya tilasta musu ficewa daga yankinsu.

“Wannan ita ce kasarsu ta asali kuma sun sadaukar da komi don su ci gaba da zama a can kuma su ci gaba da gwagwarmayar neman yancin kai,” a cewar kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran.    

Wannan kiran na Trump dai ya zo ne duk da tsananin adawar da Alkahira da Amman suka bayyana wa shirin da ya bayyana da na tsaftace yankin Gaza.

Shi dai Trump ya yi ikirarin cewa matakin na iya “kawo zaman lafiya” a yammacin Asiya idan Masar, Jordan, da sauran kasashen Larabawa suka karbi ‘yan gudun hijirar Falasdinu.

Trump ya ce tuni ya tattauna da Sarki Abdallah na biyu na Jordon kan yiwuwar gina gidaje da kuma kwashe Falasdinawa sama da miliyan daya daga Gaza.

Alkahira da Amman sun yi watsi da shawarar Trump a hukumance.

Manazarta sun ce duk wani shiri na tsugunar da Falasdinawan da suka rasa matsugunnai, zai bai wa gwamnatin Isra’ila uzurin da ta ke bukata na korar al’ummar Gaza da karfi, da kuma sake mamaye yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.

 

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori November 1, 2025 Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma