Gane sahihancin irin shuka da yake sa tsiro ya yi yabanya sosai na taka muhimmiyar rawa wajen samun girbi mai albarka, don haka wannan na’ura take da matukar muhimmanci, kana tana taimaka wa manoma su fahimci irin shukan da ya dace da yanayin yankinsu kamar yadda wani masanin ilimin injiniyancin aikin gona, Bai Lianyang ya bayyana.

Kazalika, ana ci gaba da ganin bullar fasahohin kula da gonaki ta manhajojin zamani wadanda suke sa manoma sanin halin da gonakinsu ke ciki a duk inda suke. Wani manomi dake garin Taihe a gundumar Fuyang dake lardin Anhui na gabashin kasar Sin, Chang Xinduo ya bayyana farin cikinsa game da amfani da manhajar kula da gona ta “smart agriculture cloud” wacce ta sanar da shi dirar fararen gizo-gizo da kwarin tsanya a gonarsa ta alkama, inda nan da nan ya aike da na’urar feshi mai tashi sama ta fatattake su daga gonar mai fadin ma’aunin hekta 213.

Yanzu haka dai, a garin na Taihe kawai, an samar da cibiyoyin kula da halin da gonaki ke ciki guda 20 wadanda suke iya karade gonakin alkama masu fadin ma’aunin hekta miliyan 10.14.

Ina da yakini, idan gwamnatocinmu na Afirka suka nakalci amfani da sabbin fasahohin zamani na aikin gona kamar yadda kasar Sin ke yi, sannu a hankali ba da garaje ba, girbin da manomanmu ke yi za ta zama mai albarka ninkin-ba-ninki. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Hare-haren Hizbullah Sun Jazawa HKI A Fagen Gona Asarar Dala Miliyan 108

Wani rahoto na musamman da HKI ta gudanar akan asarar da ta fuskanta sanadiyyar yaki da Hizbullah, ya bayyana cewa, a fagen aikin gona kawai sun yi asarar dalar Amurka miliyan 108 wacce ta fara daga 8 ga watan Oktoba 2023.

Kungiyar ReGrow Israel” ta ce, yakin da aka yi da Hizbullah ya yi barna gagaruma a fagen aikin gona da asarar da ta kai ta dala miliyan 108 a kan iyaka da Lebanon.

Nazarin wannan kungiyar ya kuma kara da cewa; Tun daga ranar 8 ga watan Oktoba 2023 har zuwa lokacin tsagaita wutar yaki a karshen 2024, hare-haren Hizbullah sun lalata muhimmacin cibiyoyi a “Isra’ila” da kuma haddasa gobara mai girma, da hakan ya tilastawa mazaunan yankin, musamman manoma yin hijira.

Bugu da kari, binciken ya ce, barnar da yakin ya haddasa akan gonaki, ya haddasa koma baya a fagen samar da abinci, da kuma kawar da daidaito a kasuwanni.

Shugabar zartarwa ta kungiyar “ReGrow Isra’el” Danil Abraham,  ta sanar da cewa; Barnar da aka samu a kan iyaka da Lebanon tana da girman gaske, da kuma rikiritarwa, ta kuma shafi yanki mai girma fiye da fagen dagar Gaza.

Abraham ta kuma ce; Sai 9000 aka kai wa arewacin “HKI” hare-hare da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki, da hakan ya sa gonaki masu yawa su ka kone. Haka nan kuma kaso 60% na manoman a Arewacin HKI, sun dakatar da ayyukansu baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Siriya Tana Neman Tattaunawa Da Gwamnatin Mamayar Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Ma’aunin Asusun Ajiyar Kudin Musayar Waje Na Sin Na Cikin Daidaito
  • An gabatar da sabbin shaidu kan Nnamdi Kanu
  • Jagora: Muhimmin Aikin Makarantar “Hauza” Shi ne Isar Da Sakon Addini
  •  Hare-haren Hizbullah Sun Jazawa HKI A Fagen Gona Asarar Dala Miliyan 108
  • APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
  • Karuwar Tafiye-Tafiye Yayin Hutun Ranar Ma’aikata A Kasar Sin Ya Bayyana Kuzarin Masu Kashe Kudi
  • Hamas : Tattaunawar sulhu ba ta da wani tasiri a halin da ake ciki
  • ’Yan fashi sun kashe matashi a Kano