Aminiya:
2025-05-21@20:59:43 GMT

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta

Published: 17th, April 2025 GMT

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da gwamnatin Najeriya.

Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.

Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary Yaou Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba  Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.

Allah Ne Ya haɗa wannan zumunta ka, babu wanda ya isa ya raba ta.”

Takwaransa na Najeriya, Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa nan gaba Shugaba Bola Ahmed Tinubu za su gana da shugaban gwamnatin sojin Nijar, Janar Abdurrahman Tchiani, a matsayin ci gaban wannan daidaitawa.

Ya bayyana cewa yarjejeniyar da ƙasashen biyu suka sanya hannu a kai, ta zama, “darasi ga duk wasu ƙasashen duniya, domin yanzu an shiga wani lokaci da ake fama da tashe tashen hankali. To yanzu mu abin da a muka a tsakaninmu ya zama abin koyi.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai

এছাড়াও পড়ুন:

DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 

Ya ce, “Eh, an kama Galadi yau yayin da ake tantance shi da nufin zuwa Saudiyya.”

Kama Galadi na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan kama wani riƙaƙƙen ɗan bindiga a sansanin alhazai da ke Abuja.

Ana zargin mutumin da hannu a wasu manyan sace-sacen mutane a Jihar Kogi da Abuja.

An shiga ruɗani yayin da wasu ke tambayar yadda mutanen da ake nema ke samun damar mallakar takardun tafiye-tafiye da wuce matakan tsaro ba tare da an gano su ba.

Amma jami’in DSS ya ce wannan tambaya ta shafi sauran hukumomi da ke bayar da fasfo da kula da tafiye-tafiye.

Ya ƙara da cewa, “Galadi yana hannunmu yanzu kuma yana amsa tambayoyi. Za a gurfanar da shi a kotu bayan an kammala bincike.”

ya zuwa yanzu dai babu wata sanarwa daga gwamnatin jihar ko wata hukumar tsaro game da kama Galadi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Yan Siyasa A Burtaniya Suna Matsaya Gwamnatin Kasar Ta Amince Da Kasar Falasdinu
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin ZamfaraBabu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON
  • Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun
  • DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 
  • Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON
  • An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za Ku Kula Da Lafiyar Jikinku
  • NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?