Aminiya:
2025-11-22@00:30:58 GMT

Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu

Published: 13th, April 2025 GMT

Tsohon ɗan wasa, kuma tsohon mai horas da ’yan ƙwallon Super Eagles ta Najeriya, Christian Chukwu ya rasu.

Christian Chukwu ya rasu ranar Asabar yana da shekara 74.

Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato

Christian Chukwu ne kyaftin ɗin tawagar Super Eagles lokacin da Najeriya ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON) ta 1980.

Dakta Olusegun Odegbami, tsohon ɗan wasan Najeriya kuma abokin Chukwu, ya tabbatar rasuwar mai ban tausayi a saƙon da ya wallafa ta manhajar sada zumunta X.

“Na samu labarin cewa tsakanin ƙarfe 9:00 zuwa 10:00 na safiyar yau Asabar, Christian Chukwu, MFR, wanda aka fi sani da Chairman abokina kuma abokin wasana, ɗaya daga cikin manyan ’yan wasan ƙwallon ƙafa a tarihin Najeriya, ya rasu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Super Eagles ta Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana 47 da ke faɗin Najeriya.

Gwamnatin ta ɗauki wannan mataki ne bayan hare-haren da ’yan bindiga suka kai makarantu a jihohin Kebbi da Neja, inda suka sace ɗalibai da ma’aikata, suka kashe mutum ɗaya.

Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja

A wata takarda da aka aike wa shugabannin makarantu a ranar Juma’a, Daraktar Makarantun Sakandare, Hajiya Binta Abdulkadir, ta ce Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, ya amince da rufe makarantun na wucin gadi saboda barazanar matsalolin tsaro.

Takardar ta bayyana cewa an rufe makarantun ne domin kare ɗalibai da malamai daga hare-haren ’yan bindiga, da kuma kauce wa duk wata barazana.

Makarantun da abin ya shafa sun haɗa da waɗanda ke Zariya, Daura, Sakkwato, Potiskum, Ikare-Akoko, Abaji, da sauransu.

Wannan umarni na zuwa ne a daidai lokacin da hare-haren da ake kai wa makarantu ke ƙara tsananta.

A Jihar Kebbi, ’yan bindiga sun kai hari makarantar Government Girls Comprehensive Secondary School da ke Maga, inda suka sace ɗalibai 25, tare da kashe mataimakin shugaban makarantar, Malam Hassan Makaku, yayin da yake ƙoƙarin kare su.

Rahotanni sun nuna cewa daga 2014 zuwa 2022, an sace yara sama 1,680 a makarantun Najeriya.

Gwamnati ta ce rufe makarantun na wucin gadi ne, domin kare ɗalibai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki
  • Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Hakimi ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana
  • Osimhen ba zai halarci bikin karrama gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana ba
  • Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
  • Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya