Aminiya:
2025-10-23@01:33:28 GMT

Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu

Published: 13th, April 2025 GMT

Tsohon ɗan wasa, kuma tsohon mai horas da ’yan ƙwallon Super Eagles ta Najeriya, Christian Chukwu ya rasu.

Christian Chukwu ya rasu ranar Asabar yana da shekara 74.

Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato

Christian Chukwu ne kyaftin ɗin tawagar Super Eagles lokacin da Najeriya ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON) ta 1980.

Dakta Olusegun Odegbami, tsohon ɗan wasan Najeriya kuma abokin Chukwu, ya tabbatar rasuwar mai ban tausayi a saƙon da ya wallafa ta manhajar sada zumunta X.

“Na samu labarin cewa tsakanin ƙarfe 9:00 zuwa 10:00 na safiyar yau Asabar, Christian Chukwu, MFR, wanda aka fi sani da Chairman abokina kuma abokin wasana, ɗaya daga cikin manyan ’yan wasan ƙwallon ƙafa a tarihin Najeriya, ya rasu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Super Eagles ta Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Pillars ta dakatar da Kocinta

Hukumar gudanarwar Kungiyar Kwallon kafa ta Kano Pillars ta dakatar da Babban Kocinta Ahmed Garba Yaro Yaro da bai ba da shawara ga  Kocin, Ogenyi Evans, nan take.

Ta kuma nada tsohon kyaftin kuma Mataimakin Koci, Gambo Muhammad nan take, ya jagoranci lamuran fasaha na ƙungiyar. Mai horar da masu tsaron raga, Suleiman Shuaibu, zai taimaka masa, yayin da Koci Garzali Muhammad (Kusa) daga Junior Pillars zai ba da ƙarin goyon baya har sai an fitar da sabbin umarni.

Kungiyar ta dauki wannan mataki ne bayan abin da ta kira “rashin tagomashinta” a Gasar Firimiyar Najeriya (NPFL) ta 2025/2026 da ake ci gaba da yi.

Sanarwa da kulob ɗin ta fitar, hukumar gudanarwar ta ce an ɗauki matakin ne bayan nazarin yadda ƙungiyar ta yi rashin nasara a wasannin ta na baya-bayan nan.

Ta ce “Yanzu haka, ’yan wasan sun buga wasanni takwas, amma nasara biyu kacal suka samu a ciki, sun yi canjaras biyu, sannan kuma an doke su a wasanni huɗu.”

An kama ɗan uwan Nnamdi Kanu da lauyansa —Sowore Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamna da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya

Kulob ɗin, wanda yana ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da suka fi rawar gani a tarihin ƙwallon ƙafa a Najeriya, yana fama da rashin daidaituwa a wannan kakar, abin da ke tayar da hankalin magoya baya da masu ruwa da tsaki kan jagorancin ƙungiyar.

Sanarwar ta tabbatar wa magoya baya cewa hukumar gudanarwar ta ci gaba da jajircewa wajen dawo da ƙungiyar kan turba da kuma dawo da dabi’ar ta ta samun nasara.

Kano Pillars, wadda aka fi sani da ‘Sai Masu Gida’, a halin yanzu tana can ƙasan teburin gasar ta NPFL, kuma tana fatan samun canji mai kyau yayin da kakar ke ci gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a fashewar tanka a Neja
  • Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 
  • Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Muka Shiga Sakamakon Haihuwar ’Ya Mai Cutar Motsewar Kwakwalwa
  • Dan Wasan Barkwanci A Finafinan Indiya, Asrani Ya Rasu
  • Yadda Morocco ta kafa tarihin ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20
  • Kano Pillars ta dakatar da Kocinta
  • Kotu A Faransa Ta Yanke Hukumci Zama Gidan Yari Ga Tsohon Shugaban Kasar Nicola Sarkozi
  • Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamnan da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?