NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
Published: 11th, April 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A Najeriya ana tafka muhawara a kan yadda farashin ɗanyen man fetur yake ƙara faduwa a kasuwannin duniya.
Wannan lamari dai ya haddasa damuwa a zukatan wasu ’yan ƙasar, kama daga masana tattalin arziki zuwa jami’an gwamnati, kasancewar ɗanyen mai ne mafi muhimmanci a cikin hanyoyin samun kuɗaɗen shigar ƙasar.
Sai dai tambayar da wasu ’yan kasar suke yi ita ce: shin yaya wannan faɗuwar ta farashin ɗanyen mai za ta shafi rayuwar talaka?
NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’Shirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan yadda faɗuwar farashin ɗanyen man fetur zai shafi ɗan Najeriya.
Domin sauke shirin, latsa nan: https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16955648-yadda-fa-uwar-farashin-anyen-mai-zai-shafi-rayuwar-yan-najeriya.mp3?download=true
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ɗanyen mai faɗuwar farashi Najeriya Rayuwar Talaka
এছাড়াও পড়ুন:
Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
Dakarun Sojin Amurka sun kammala shirye-shiryen kai hare-hare a Najeriya bayan umarnin da Shugaba Donald Trump, ya bai wa Ma’aikatar Tsaron ƙasar kan ɗaukar mataki game da zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.
Jaridar The New York Times ta ruwaito cewa rundunar sojin Amurka da ke nahiyar Afirka (AFRICOM), ta gabatar da yadda hare-haren za su kasance.
An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwaDaga cikin shirin akwai kai wa ’yan ta’adda hare-hare da jiragen yaƙi da amfani da jirage marasa matuƙa.
Sannan kuma akwai tsarin haɗin gwiwa da sojojin Najeriya ta hanyar musayar bayanan leƙen asiri da tallafin kayan aiki.
Sai dai jami’an Ma’aikatar Tsaron Amurka sun yi gargaɗin cewa irin waɗannan hare-haren ba lallai su magance matsalolin tsaro a Najeriya ba.
Sun ce dole sai an gudanar da yaƙi mai faɗi kamar yadda aka yi a Iraƙi ko Afghanistan, sai dai sun ce hakan zai sa Amurka ta kashe maƙudan kuɗaɗe.
Trump, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da tin sakaci wajen “kisan Kiristoci,” kuma ya bayar da umarnin dakatar da sayar wa Najeriya makamai.
Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata zargin, inda ta danganta matsalar tsaro da wasu abubuwa kuma tana shafar kowane ɓangare na addini.
Mai bai wa Shugaba Tinubu shawara, Daniel Bwala, ya bayyana cewa Najeriya ba ta buƙatar sojojin Amurka su shiga ƙasarta, sai dai taimako a fannin leƙen asiri da kayan aiki, tare da buƙatar Amurka ta mutunta Najeriya.
Ƙasar China ta goyi bayan Najeriya, tare da gargaɗin Trump kan tsoma baki cikin harkokin da suka shafi ƙasa mai ’yanci.
Masana da tsofaffin Hafsoshin sojin Amurka sun yi gargaɗin cewa irin wannan farmaki zai iya ƙara ta’azzara matsalar tsaro.
Sun kuma bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ta samo asali ne daga ’yan fashi, rikicin filaye, da ta’addanci da ke shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.