More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A Najeriya ana tafka muhawara a kan yadda farashin ɗanyen man fetur yake ƙara faduwa a kasuwannin duniya.

Wannan lamari dai ya haddasa damuwa a zukatan wasu ’yan ƙasar, kama daga masana tattalin arziki zuwa jami’an gwamnati, kasancewar ɗanyen mai ne mafi muhimmanci a cikin hanyoyin samun kuɗaɗen shigar ƙasar.

Sai dai tambayar da wasu ’yan kasar suke yi ita ce: shin yaya wannan faɗuwar ta farashin ɗanyen mai za ta shafi rayuwar talaka?

NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Shirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan yadda faɗuwar farashin ɗanyen man fetur zai shafi ɗan Najeriya.

Domin sauke shirin, latsa nan: https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16955648-yadda-fa-uwar-farashin-anyen-mai-zai-shafi-rayuwar-yan-najeriya.mp3?download=true

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗanyen mai faɗuwar farashi Najeriya Rayuwar Talaka

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye ta hanyar hadin gwiwa da inganta fasaha.

 

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris ne ya bayar da wannan tabbacin a taron manema labarai na 2025 da aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta kasa da ke Abuja ranar Alhamis.

 

Da yake jawabi bayan dawowar sa daga taron kungiyar masu yada labarai na duniya (NAB) a birnin Las Vegas na kasar Amurka, ministan ya ce taron mai taken “Fasahar, The Trend, The Future,” ya samar da wani dandali na yin cudanya da masu ruwa da tsaki a duniya kan sabbin abubuwa da suka tsara makomar watsa shirye-shirye.

 

Ya ce shigarsa wani bangare ne na kokarin da gwamnatin Tinubu ke yi na bunkasa fasahar na bangaren yada labarai na Najeriya.

 

A cewarsa, “wannan zai tabbatar da kudurin gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an samu sauyi mai dorewa a fagen yada labaran Najeriya.”

 

Ministan ya kuma bayyana irin rawar da ya taka a taron ‘yan kasuwan Najeriya da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa, inda ya gana da jami’an UNESCO kan shirin kafa cibiyar koyar da kafafen yada labarai da wayar da kan jama’a a Abuja. Ana sa ran Cibiyar da aka tsara za ta inganta tare da samarda ƙwararrun ‘yan jarida da haɓaka ayyukan watsa labarai masu dacewa.

 

Ya kuma kara jaddada cewa shirin gabatar da jawabai na ministocin da ake yi da kuma tarukan da aka shirya yi a fadin kasar nan na da nufin tabbatar da gaskiya, hada kan jama’a, da kara dankon zumunci tsakanin gwamnati da ‘yan kasa.

 

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, wanda ya bayyana muhimman ci gaban da aka samu a fannin samar da wutar lantarki, wanda ya yi daidai da ajandar gwamnati na bunkasa masana’antu a Najeriya da inganta samar da wutar lantarki a fadin kasar.

 

Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • Yadda Za Ku Hada ‘Mimi Fankek’
  • NAJERIYA A YAU: Sabbin dabarun hana matasa aikata laifi
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)
  • Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Yadda Hukuncin Kotun Koli Ya Kara Dagula Rikicin Shugabanci A PDP Da LP
  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta
  • Fani-Kayode ya zargi Isra’ila da Hannu a tashe-tashen hankula a Najeriya