More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A Najeriya ana tafka muhawara a kan yadda farashin ɗanyen man fetur yake ƙara faduwa a kasuwannin duniya.

Wannan lamari dai ya haddasa damuwa a zukatan wasu ’yan ƙasar, kama daga masana tattalin arziki zuwa jami’an gwamnati, kasancewar ɗanyen mai ne mafi muhimmanci a cikin hanyoyin samun kuɗaɗen shigar ƙasar.

Sai dai tambayar da wasu ’yan kasar suke yi ita ce: shin yaya wannan faɗuwar ta farashin ɗanyen mai za ta shafi rayuwar talaka?

NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Shirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan yadda faɗuwar farashin ɗanyen man fetur zai shafi ɗan Najeriya.

Domin sauke shirin, latsa nan: https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16955648-yadda-fa-uwar-farashin-anyen-mai-zai-shafi-rayuwar-yan-najeriya.mp3?download=true

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗanyen mai faɗuwar farashi Najeriya Rayuwar Talaka

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Da yake ƙarin haske kan muhimman sassan da aka fi bai wa fifiko, Gwamnan ya bayyana cewa, ɓangaren tattalin arziƙi da ci gaban al’umma ne suka samu kaso mafi tsoka na kasafin kuɗin, inda aka ware sama da Naira biliyan 269 don sanya hannun jari a muhimman fannoni.

Fannin ayyuka, gidaje da sufuri ne ke kan gaba da Naira Biliyan 135.9, sai ruwa, muhalli da gandun daji da aka warewa Naira Biliyan 88.4, yayin da noma, kiwo da ƙungiyoyin gama ya samu Naira biliyan 20.57.

A fannin harkokin zamantakewa, an ware Naira biliyan 80 don samar da ayyukan ci gaba da gina jama’a, inda ilimi ya samu Naira biliyan 31.9, yayinda ilimi mai zurfi ya samu Naira biliyan 17.5.

Ɓangaren kiwon lafiya ya samu Naira biliyan 25.9, wanda hakan ke nuna yadda gwamnati ke ci gaba da zuba jari wajen samar da lafiya mai inganci.

Fannin gudanarwa ya samu Naira biliyan 19.63, sannan ɓangaren doka da shari’a aka ware masa Naira biliyan 2.17, fannin filaye ya samu Naira biliyan 6.46; shi kuwa fannin Kasuwanci, Masana’antu da Yawon Buɗe Ido ya samu Naira biliyan 4.02.

Yayin da sashen matasa da ci gaban wasanni ya samu Naira biliyan 3.33; harkokin mata da ci gaban a’umma Naira biliyan 1.28; fannin yaɗa Labarai da raya al’adu kuwa Naira biliyan 10.38.

Gwamna Yahaya ya bayyana ƙididdigar kasafin kuɗin na 2026 a matsayin na ɗorawa kan ci gaban da gwamnatinsa ta faro na gudanar da shugabanci nagari, Gwamna Inuwa Yahaya ya yi ƙira ga majalisar akan ta yi nazari tare da ƙalailaice ƙudurin tare da sanya gudunmawa da tabarrukinta.

“Aikin dake gabanmu shi ne mu samarwa al’ummarmu kasafin kuɗin da zai wanzar da fatansu ya zuwa zahiri da kuma kyautata makomarsu,” in ji shi.

Kasafin kuɗin na 2026 ya dace da tsarin ci gaban Jihar Gombe (DEVAGOM) da kuma tsarin tattalin arziƙin ƙasa baki ɗaya. Da yake tsokaci kan harkokin tattalin arziƙi a dunƙule, Gwamnan ya ce sauye-sauyen da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ɓullo da su, da suka haɗa da cire tallafin man fetur da sakin mara ga canjin kuɗaɗen waje, sun fara haifar da sakamako na ƙwarai.

A nasa jawabin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Gombe Rt. Hon. Muhammad Abubakar Luggerewo, ya yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da bin doka da oda, da gaskiya da kuma tsantseni wajen tafiyar da harkokin kuɗaɗen gwamnati.

Ya bada tabbacin duba kasafin akan lokaci da kuma gaggauta amincewa da ƙudurin kasafin na 2026.

Rt. Hon. Luggerewo ya kuma nuna jin daɗinsa da yadda jihar ke tafiyar da harkokin kasafin kuɗi, inda ya ce aiwatar da kasafin kuɗin 2025 ya samu nasarar fiye da kaso 60 cikin 100 ya zuwa ƙarshen watan Satumba, sannan ya yaba da yadda gwamnati ta samu ci gaba a fannin samar da ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, masana’antu, da sabunta birane.

“Za mu ci gaba da tallafawa manufofi da tsare-tsaren dake tabbatar da zaman lafiya, inganta ci gaban tattalin arziki da kyautata rayuwar jama’armu,” in ji kakakin.

A shekarar da ake ciki ta 2025, Gwamnatin Inuwa ta yi kasafi ne na fiye da Naira biliyan 369.9, inda daga baya aka yi bitarsa ya koma na fiye da Naira biliyan 451.6 biyo bayan samun ƙarin kuɗaɗen shiga fiye da yadda aka yi tsammani.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani November 14, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70 November 14, 2025 Manyan Labarai Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN November 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Yadda Babban Taronjam’iyyar PDP ke gudana
  • Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya
  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
  • An kama ’yan Najeriya 3 a Kenya kan zargin aikata damfara
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani
  • Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar Kano
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • Majalisa ta amince da buƙatar Tinubu na karɓo rancen N1.15bn
  • Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa