Aminiya:
2025-11-03@01:59:00 GMT

Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas

Published: 21st, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi caccaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas.

Kwankwaso ya ce matakin da Tinubu ya ɗauka ya saɓa doka kuma barazana ne ga dimokuraɗiyya.

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Kwankwaso ya gargaɗi cewa irin wannan matakin na iya kafa mummunan misali da kuma illata dimokuraɗiyya a Najeriya.

Kwankwaso, ya ruwaito yadda rikicin siyasa da ya haifar da soke zaɓen 1993, inda ya jaddada cewa ‘yan majalisa su daina ɓata lokacinsu kan abubuwan da ba su dace ba.

“Majalisa tana da alhakin sa ido kan ayyukan ɓangaren zartarwa, ba wai kawai yarda da duk abin da ta ce ba.

“Abu ne mai matuƙar tayar da hankali ganin yadda Majalisar Tarayya ta 10 ta fi kowace zama ‘yar amshin shata ga ɓangaren zartarwa,” in ji shi.

Tsohon gwamnan ya kuma soki yadda Majalisar Tarayya ta gaggauta amincewa da matakin Shugaba Tinubu ba tare da bin ƙa’idojin da kundin tsarin mulki ya tanada ba.

“Kundin tsarin mulki ya fayyace yadda ake yanke hukunci kan irin wannan matsala, amma ‘yan majalisa sun zaɓi amfani da murya wajen zaɓe, wanda hakan yana janyo shakku kan sahihancin lamarin.

“Gaggawar amincewa da dokar ta-ɓaci da zata kifar da gwamnatin da aka zaɓa, cin fuska ne ga dimokuraɗiyya,” in ji shi.

Kwankwaso ya kuma yi gargaɗi kan shigar sojoji cikin harkokin mulki, inda ya bayyana cewa hakan tamkar komawa baya ne bayan ci gaban da aka samu tsawon shekaru 26 na dimokuraɗiyya.

Ya bayyana damuwarsa cewa wannan matakin na iya zama wata dabara ta murƙushe jihohin da ba sa tare da jam’iyya mai mulki.

“A matsayinsa na wanda ke da’awar kare dimokuraɗiyya, Shugaba Tinubu ya kamata ya fi kowa fahimta cewa kawo sojoji cikin mulki hatsari ne.

“Wannan matakin ba wai kawai barazana ne ga zaman lafiya ba, yana iya zama hanyar kama-karya idan ba a dakatar da shi ba,” in ji Kwankwaso.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Kwankwaso Kwankwaso ya

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

“Amurka ba za ta tsaya kawai tana kallo ba yayin da irin waɗannan ta’addancin ke faruwa a Nijeriya da sauran ƙasashe.

“Mun shirya, muna da ƙarfi da niyyar kare Kiristoci a faɗin duniya,” in ji Trump.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano October 31, 2025 Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazanar Sa Ga Nijeriya
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari