Dabarun Kasar Sin Na Iya Kawo Karshen Yunwa A Duniya
Published: 18th, March 2025 GMT
A baya-bayan nan yayin hira da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ministan kula da harkokin gona na kasar Gambiya Demba Sabally, ya bayyana goyon baya da taimakon fasaha na kasar Sin, a matsayin wadanda suka taka muhimmiyar rawa wajen samar da gagarumin ci gaba a fannin aikin gona a kasarsa a ’yan shekarun nan.
Idan ana batu na kirkira da amfani da fasahar zamani a duniya, to kowa ya san cewa kasar Sin ta yi zarra a wannan bangare. Haka kuma kowa ya san duk wani ci gaban da Sin take nema ko ta samu, tana yi ne domin jama’arta su kasance cikin walwala, shi ya sa ci gaban Sin a fannin kirkire-kirkiren fasahohin zamani, ya game kowane bangare na rayuwa, ciki har da ayyukan gona. Kasar Sin daya ce daga cikin kasashe mafiya yawan jama’a a duniya, amma jajircewarta da dabarunta, sun ba ta damar ciyar da daukacin al’ummarta, duk da cewa, ba ta da filin noma mai yawa.
Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya Gwamna Yusuf Ya Yi Barazanar Ƙwace Lasisin Jerin Gidajen Kwankwasiyya, Amana Da BandirawoHakika dabarun Sin abun koyi ne, musamman yadda kasar ke jajircewa wajen ganin ta taimakawa kasashe masu tasowa. Yayin da ake fama da tarin matsaloli a duniya, ciki har da rashin abinci, rungumar dabarun da matakan kasar Sin ba makawa za su samar da wadatar abinci a duniya. Kasashe da dama sun gwada kuma sun samu sakamakon a zo a gani. Misali, dalilin kasar Sin da fasahar tagwaita irin shinkafa, kasar Madagascar ta cimma burinta na samun wadatar abinci, inda a yanzu yabanyar da ake samu ta rubanya ta baya fiye da sau 1. Ita ma kasar Gambia, yawan yabanyar da take samu na ci gaba da karuwa, inda yawan shinkafar da kasar ta samu a shekarar 2024 ya haura tan 48,000, adadin da ya kafa tarihi.
Har kullum, kasar Sin ta kasance mai rajin neman ci gaba na bai daya a duniya maimkon bai wa kanta fifiko. Hakan ne kuma ya sa take gabatar da dabaru da fasahohinta ga kasashe masu tasowa, wanda ke haska burinta na gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama, wanda muke sa ran za ta kai ga samar da wadata da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin duniya. (Faeza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
JMI ta zama zakara a gasar damben girgajiya ta kasa da kasa bayan ta fara shiga gasar shekaru 12 da suka gabata .
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi yana taya tawagar yan damben murna da nasarar da suka samu, ya kumakara da cewa wannan shi ne nasara ta wasannan kasa-da kasa har guda 6 wadanda Iran take samun lambobin zakara a cikinsu a wannan shekarar.
Labarin ya kara da cewa yan damben Iran sun sami wannan nasarar kwana guda kafin a kammala gasar.
An bayyana nasarar da yan damben Iran suka samu ne a jiya Litinin da yamma a birnin Zagreb inda aka gudanar da gasar. Sun sami lambobin yaboguda 5 a gasar wanda ya basu damar lashe gasar.
Labarin ya kara da cewa tawagar yan damben Iran sun shiga gasar ne shekaru 12 da suka gabata, kuma Amir Hussain Zare ya fita da lambar zinari a dambe mai nauyin kilogram 125.
Bayan ya sami nasara a kan dan wasan Amurka. Ahmad Mohammadnejad-Javan Azurfa daya sannan Kamran Ghasempour (86kg), da Amirhossein Firoozpour (92kg). Mohammad Nahodi da
tagulla 3.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci