Leadership News Hausa:
2025-07-03@02:55:27 GMT

Dabarun Kasar Sin Na Iya Kawo Karshen Yunwa A Duniya

Published: 18th, March 2025 GMT

Dabarun Kasar Sin Na Iya Kawo Karshen Yunwa A Duniya

A baya-bayan nan yayin hira da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ministan kula da harkokin gona na kasar Gambiya Demba Sabally, ya bayyana goyon baya da taimakon fasaha na kasar Sin, a matsayin wadanda suka taka muhimmiyar rawa wajen samar da gagarumin ci gaba a fannin aikin gona a kasarsa a ’yan shekarun nan.

Idan ana batu na kirkira da amfani da fasahar zamani a duniya, to kowa ya san cewa kasar Sin ta yi zarra a wannan bangare. Haka kuma kowa ya san duk wani ci gaban da Sin take nema ko ta samu, tana yi ne domin jama’arta su kasance cikin walwala, shi ya sa ci gaban Sin a fannin kirkire-kirkiren fasahohin zamani, ya game kowane bangare na rayuwa, ciki har da ayyukan gona. Kasar Sin daya ce daga cikin kasashe mafiya yawan jama’a a duniya, amma jajircewarta da dabarunta, sun ba ta damar ciyar da daukacin al’ummarta, duk da cewa, ba ta da filin noma mai yawa.

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya Gwamna Yusuf Ya Yi Barazanar Ƙwace Lasisin Jerin Gidajen Kwankwasiyya, Amana Da Bandirawo 

Hakika dabarun Sin abun koyi ne, musamman yadda kasar ke jajircewa wajen ganin ta taimakawa kasashe masu tasowa. Yayin da ake fama da tarin matsaloli a duniya, ciki har da rashin abinci, rungumar dabarun da matakan kasar Sin ba makawa za su samar da wadatar abinci a duniya. Kasashe da dama sun gwada kuma sun samu sakamakon a zo a gani. Misali, dalilin kasar Sin da fasahar tagwaita irin shinkafa, kasar Madagascar ta cimma burinta na samun wadatar abinci, inda a yanzu yabanyar da ake samu ta rubanya ta baya fiye da sau 1. Ita ma kasar Gambia, yawan yabanyar da take samu na ci gaba da karuwa, inda yawan shinkafar da kasar ta samu a shekarar 2024 ya haura tan 48,000, adadin da ya kafa tarihi.

Har kullum, kasar Sin ta kasance mai rajin neman ci gaba na bai daya a duniya maimkon bai wa kanta fifiko. Hakan ne kuma ya sa take gabatar da dabaru da fasahohinta ga kasashe masu tasowa, wanda ke haska burinta na gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama, wanda muke sa ran za ta kai ga samar da wadata da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin duniya. (Faeza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kakkausar Suka Kan Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta IAEA

Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA

A wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho da takwaransa na Faransa Emmanuel Macron a yammacin jiya Lahadi, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da dabi’ar nuna fuska biyu daga Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya, yana mai cewa irin wannan dabi’a ta nuna fuska biyu za ta janyo rugujewa da haifar da matsaloli da dama ga tsaron yankin da ma duniya baki daya.

A yayin wannan tattaunawa, shugaba Pezeshkian ya ce, wadannan ayyuka na nuna fuska biyu sun haifar da matsaloli da dama ga harkokin tsaro na yanki da na duniya, kuma ana sa ran hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA za ta mutunta haƙƙin kasashe da guje wa ɗabi’a nuna fuska biyu a fagen ayyukanta da kuma kare haƙƙin ƙasashe membobinta.

A martanin da shugaban kasar Faransa ya nuna dangane da matakin Iran na dakatar da hadin gwiwa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, shugaba Pezeshkian ya soki yadda babban sakataren hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA ke bayar da rahotannin da ba su dace ba kan shirin makamashin nukiliyar Iran da kuma rashin yin Allah wadai da harin da aka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, wanda ya saba wa dokokin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
  • Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
  • Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kakkausar Suka Kan Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta IAEA
  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya