‘Yan Jarida Muhimman Ginshiƙai Ne A Tsakanin Al’umma Da Gwamnati – Gwamnatin Nasarawa
Published: 13th, March 2025 GMT
Magaji ya yaba wa ‘yan jarida bisa irin goyon bayan da suke bai wa gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule.
Ya ce gwamnatin jihar na ci gaba da ayyukan ci gaba da kuma inganta abubuwan da gwamnatoci na baya suka aiwatar.
Haka kuma, ya shawarci ‘yan jarida da su tabbatar da tantance labarai kafin su watsa su, domin tabbatar da sahihanci da ingancin aikin jarida.
Da yake ƙarin bayani, ya ce gwamnatin Abdullahi Sule ta kawo sauye-sauye masu amfani, musamman wajen inganta harkar haƙar ma’adinai a jihar.
Ya bayyana cewa Jihar Nasarawa ce ke kan gaba a Naieriya wajen samar da ma’adinan Lithium, wanda ke amfani ga ci gaban tattalin arziƙi.
A nasa jawabin, Shugaban ‘Yan Jarida na Jihar, Kwamared Isaac Ukpoju, ya bayyana cewa sun kai ziyarar ne domin taya sabon Sakataren Gwamnatin Jihar murna bisa naɗin da aka yi masa.
Ya ce naɗin da aka yi wa Labaran Shuaibu Magaji ya dace da shi, kuma ‘yan jarida ba su yi mamaki ba duba da irin tarihin ayyukansa.
Haka kuma, ya roƙi Sakataren Gwamnatin da ya haɗa su cikin harkokin yaɗa labarai na gwamnati, musamman a ɓangaren tallafa wa ayyukansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Jarida Nasarawa Sakataren gwamnati
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kamaru Ta Gargadi Dan Takarar Da Ya Shelanta Kansa A Matsayin Wanda Ya Lashe Zabe
Ministan Harkokin Cikin Gida Ya Yi Watsi Da Shelanta Samun Nasara Da Dantakara Isa Bakari Ya Yi
Ministan harkokin cikin gidan kasar Kamaru Paul Atanga Nji ya yi watsi da yadda dan takarar shugabancin kasar Isa Tchiroma Bakari ya shelanta kansa a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa, ya kuma yi kira ga shugaban kasar Paul Biya da ya amince da shan kaye.
Ministan harkokin cikin gidan na kasar Kamaru ya zargi Issa Bakari da cewa yana da wani shiri na kokarin kona kasar Kamaru ta hanyar taimakon kasashen waje.
A makon da ya shude ma dai Atanga Nji ya yi gargadi kar wanda ya fitar da sakamakon zaben, domin yin hakan zai zama daidai da cin amanar kasa.
A karkashin dokokin zabe na kasar Kamaru kotun tsarin Mulki ce kadai take da hakkin sanar da sakamakon zabe.
A ranar 12 ga watan nan na Oktoba ne dai Issa Tchiroma ya bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi na shugaban kasa.
Shi dai Tchiroma wanda yake cikin shekaru na 70, ya taba rike mukamin mai Magana da yawun gwamnati, haka nan kuma ministan samar da ayyuka a karkashin gwamnatin Paul Biya.
Paul Biya wanda ya haura shekaru 90, ya kwashe shekaru 40 akan karagar Mulki da hakan ya mayar da shi shugaba na biyu a kasar ta Kamaru tun bayan samun ‘yanci daga Faransa. Ya hau karagar Mulki ne dai a 1982, bayan da ya kwace Mulki a hannun Ahmad Ahidjo da ya tafi waje neman magani.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar NAM Sun Nuna Goyon Bayansu Ga Venezuela October 16, 2025 Sojojin Pakistan Sun Tarwatsa Tankokin Yaki 6 Na Afghanistan A Rikicin kan Iyaka October 15, 2025 Tawagar Super Eagles Ta Nijeriya Ta Lallasa Benin Da ci 4-0 A Uyo October 15, 2025 Matakin Kasashen Yamma Na Maidowa Da Iran Takunkumi Ya Sabawa Doka. October 15, 2025 Kasar Indunusiya Ta Sanar Da Goyon Bayanta Ga Alummar Falasdinu October 15, 2025 Isra’ila Za Ta Sake Kai Hare-hare Idan Ta Karbi Dukkan Mutanenta Da Hamas Ta Kama. October 15, 2025 Trump Ya Fadawa Hamas Su Mika Makamansu Ko Kuma A Kwace Su Da Karfi October 15, 2025 Iran Ta Samarda Sabbin Hanyoyi Na Fuskantar Barazanar Makiya October 15, 2025 Hamas Ta Ce HKI Tana Cikas Neman Gawawwakin Yahudawa A Gaza October 15, 2025 Yansandan Italiya Sun Kara Da Masu Goyon Bayan Falasdinawa A Garin Udine October 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci