Magaji ya yaba wa ‘yan jarida bisa irin goyon bayan da suke bai wa gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule.

Ya ce gwamnatin jihar na ci gaba da ayyukan ci gaba da kuma inganta abubuwan da gwamnatoci na baya suka aiwatar.

Haka kuma, ya shawarci ‘yan jarida da su tabbatar da tantance labarai kafin su watsa su, domin tabbatar da sahihanci da ingancin aikin jarida.

Da yake ƙarin bayani, ya ce gwamnatin Abdullahi Sule ta kawo sauye-sauye masu amfani, musamman wajen inganta harkar haƙar ma’adinai a jihar.

Ya bayyana cewa Jihar Nasarawa ce ke kan gaba a Naieriya wajen samar da ma’adinan Lithium, wanda ke amfani ga ci gaban tattalin arziƙi.

A nasa jawabin, Shugaban ‘Yan Jarida na Jihar, Kwamared Isaac Ukpoju, ya bayyana cewa sun kai ziyarar ne domin taya sabon Sakataren Gwamnatin Jihar murna bisa naɗin da aka yi masa.

Ya ce naɗin da aka yi wa Labaran Shuaibu Magaji ya dace da shi, kuma ‘yan jarida ba su yi mamaki ba duba da irin tarihin ayyukansa.

Haka kuma, ya roƙi Sakataren Gwamnatin da ya haɗa su cikin harkokin yaɗa labarai na gwamnati, musamman a ɓangaren tallafa wa ayyukansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Jarida Nasarawa Sakataren gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Comoros Azali Assoumani, sun aika wa juna sakon taya murnar cika shekaru 50 da kulla alakar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu.

A cikin sakonsa, shugaba Xi Jinping ya nuna cewa, yana mayar da hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Comoros, kuma yana son hada hannu da shugaba Azali, da amfani da cikar alakar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu shekaru 50, a matsayin wata dama ta ciyar da dangantakarsu ta gargajiya gaba, da ma inganta tabbatar da nasarorin da aka cimma a yayin taron koli na Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC), da bunkasa dangantakar dake tsakanin Sin da Comoros bisa manyan tsare-tsare, da kuma kara taka rawar gani wajen gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta Sin da Afirka ta ko wane lokaci a sabon zamani.

A nasa bangaren, shugaba Azali ya bayyana cewa, bisa yanayin da duniya ke ciki na fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice, ra’ayin da shugaba Xi Jinping ya gabatar na girmama ikon mulkin kai da rashin tsoma baki cikin harkokin gidan kasa da kasa tare kuma da cimma nasara tare ta hanyar hadin kai, ya kara wa kasashe masu tasowa kwarin gwiwa, ciki har da kasar Comoros. Ya ce kasarsa na son yin kokari tare da kasar Sin bisa ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil-Adam, don karfafa samun dauwamamman ci gaba irin na hakuri da juna, da ba da gudummawa ga inganta hadin kai da ma samun wadata tare a tsakanin Afirka da Sin. (Bilkisu Xin)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe November 13, 2025 Daga Birnin Sin An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea November 13, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa November 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa
  • BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
  • Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki
  • Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 
  • Gwamna Nasarawa Ya Ce Za Su Samar da Masana’antu Don Ayyukan Yi
  • Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
  • Gwamnatin Jigawa Ta Himmatu Wajen Inganta Harkokin Kiwon Lafiya a Jihar
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa
  • Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Shirya Faɗaɗa Gonakin Shinkafar Jangwa Don Ƙara Samar da Shinkafa