Magaji ya yaba wa ‘yan jarida bisa irin goyon bayan da suke bai wa gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule.

Ya ce gwamnatin jihar na ci gaba da ayyukan ci gaba da kuma inganta abubuwan da gwamnatoci na baya suka aiwatar.

Haka kuma, ya shawarci ‘yan jarida da su tabbatar da tantance labarai kafin su watsa su, domin tabbatar da sahihanci da ingancin aikin jarida.

Da yake ƙarin bayani, ya ce gwamnatin Abdullahi Sule ta kawo sauye-sauye masu amfani, musamman wajen inganta harkar haƙar ma’adinai a jihar.

Ya bayyana cewa Jihar Nasarawa ce ke kan gaba a Naieriya wajen samar da ma’adinan Lithium, wanda ke amfani ga ci gaban tattalin arziƙi.

A nasa jawabin, Shugaban ‘Yan Jarida na Jihar, Kwamared Isaac Ukpoju, ya bayyana cewa sun kai ziyarar ne domin taya sabon Sakataren Gwamnatin Jihar murna bisa naɗin da aka yi masa.

Ya ce naɗin da aka yi wa Labaran Shuaibu Magaji ya dace da shi, kuma ‘yan jarida ba su yi mamaki ba duba da irin tarihin ayyukansa.

Haka kuma, ya roƙi Sakataren Gwamnatin da ya haɗa su cikin harkokin yaɗa labarai na gwamnati, musamman a ɓangaren tallafa wa ayyukansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Jarida Nasarawa Sakataren gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi

Saboda matsin lamba na doka da kuma la’akari da mahimman batutuwan siyasa, ya zama dole Gwamnatin Jihar Bauchi ta dakatar da duk wani ci gaba na aikin kwamitin da aka kafa a ranar 4 ga Yuli 2025 domin duba yiwuwar ƙirƙirar sabbin masarautu ko sauye-sauye ga tsarin majalisun gargajiya—musamman a yankunan da har yanzu ke fuskantar shari’a a kotu.

Ci gaba da wannan lamari mai sarkakiya alhali wasu muhimman ƙarar shari’a na ci gaba a kotuna, ba wai kawai zai saɓa wa kundin tsarin mulki da ikon shari’a ba, har ila yau, zai iya haddasa tayar da jijiyoyin wuya a cikin al’umma, musamman a yankunan da ke da tarihi na rikice-rikicen ƙabilanci kamar Tafawa Balewa da kewaye.

Wannan kira na haƙuri yana da tushe duka a doka da alhaki domin kare zaman lafiya da mutunta doka.

Shari’o’in da ke Gaban Kotu:

A bayyane yake cewa akwai manyan shari’o’i guda biyu da har yanzu ba a yanke hukunci kansu ba a Babbar Kotun Shari’a ta Jihar Bauchi, kuma akwai yiwuwar ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Jos:

Shari’o’in biyu sun haɗa da mai lamba: BA/191/2011 da ke gudana tsakanin Hon. Barr. Bukata Zhyadi da wasu 3 a ɓangare ɗaya, sai kuma Gwamnan Jihar Bauchi da wasu 15 a ɗaya ɓangaren.

Akwai kuma shari’a mai lamba: BA/173/2012 – wadda ake yi tsakanin Alhaji Maigida Abdullahi (Sarkin Tafawa Balewa) da wasu 4 a ɓangare ɗaya, da kuma Baba Garba Vurmi da wasu 7 a ɗaya ɓangaren.

Waɗannan shari’o’in suna da tushe a cikin dogon tarihin rikice-rikicen ƙabilanci a Tafawa Balewa, wanda tun daga 1959 ake fama da tarzoma lokaci zuwa lokaci, wanda ya haddasa salwantar rayuka da dukiya, sakamakon saɓani kan masarautun gargajiya, iyakokin ƙabilu da matsalolin ganewa tsakanin al’umma.

Ka’idar Haramta Tsoma Baki a Shari’ar Da ke Gaban Kotu:

Dangane da ka’idar (sub judice) wadda ta haramta tsoma baki a shari’ar da ke gaban kotu da kuma tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 (wanda aka gyara), musamman sashe na 6(6)(b) — wanda ya ba da cikakken ikon yanke hukunci ga kotuna kawai.

Sai sashe na 14(2)(b) — wanda ya bayyana tsaron lafiya da walwalar jama’a a matsayin babban dalilin kafa gwamnati,

Ya zama rashin ɗa’a a doka, rashin adalci a akhlaƙi, da kuma sakaci a siyasa, a ci gaba da wani aiki na gwamnati ko na dokar majalisa wanda zai iya kawo cikas ga hukuncin da kotu take jira.

Bugu da ƙari, Kotun Koli ta Najeriya a hukuncinta na Gwamnan Legas a zamanin mulkin soji da kuma Ojukwu (1986) 1 NWLR (Pt. 18) 621, ta tabbatar da cewa babu wani ɓangare, har da gwamnati, da ya dace ya ɗauki mataki kai-tsaye a kan batutuwan da ke gaban kotu, domin hakan na raina ikon kotu da tsarin doka.

Ƙirƙirar sabbin masarautu ko ɗaukar matakin dokoki masu sarkakiya a yankunan da ake rigima da su, na iya sake tayar da tarzoma, karya zaman lafiya da rushe ƙoƙarin da aka daɗe ana yi na sasanta rigingimu a Kudancin Bauchi.

Shawarwari:

i) Gwamnatin Jihar Bauchi, Majalisar Zartarwa da Majalisar Dokoki su dakatar da duk wani tunani ko mataki kan ƙirƙirar sabbin masarautu ko sauya tsarin majalisun gargajiya a yankunan da abin ya shafa;

ii) Hukumomin tsaro da ƙungiyoyin wanzar da zaman lafiya su kasance cikin shiri da lura da duk wani yunƙuri da zai iya haddasa rikici a cikin al’umma;

iii) Sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin al’umma da dattawan yankuna su tallafa wa bin doka da tafiyar da mulki bisa zaman lafiya.

Kammalawa:

Gwamnatin Jihar Bauchi ya kamata ta tuna cewa matakin da aka ɗauka cikin gaggawa ko wulaƙanta tsarin shari’a, na iya fuskantar soke daga kotu, kuma illar hakan ga rayukan al’umma da hadin kai na jama’a ba za a iya aunawa ba.

A bar kotu ta yanke hukunci. A bar zaman lafiya ya ɗore.

Saƙo daga Mukhtar Abubakar Tafawa Balewa Bauchi, Najeriya

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kenya: Zanga-zanga Ta Tsayar Da Kai Komo A Birnin Nairobi
  • Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi
  • Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
  • Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila