‘Yan Jarida Muhimman Ginshiƙai Ne A Tsakanin Al’umma Da Gwamnati – Gwamnatin Nasarawa
Published: 13th, March 2025 GMT
Magaji ya yaba wa ‘yan jarida bisa irin goyon bayan da suke bai wa gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule.
Ya ce gwamnatin jihar na ci gaba da ayyukan ci gaba da kuma inganta abubuwan da gwamnatoci na baya suka aiwatar.
Haka kuma, ya shawarci ‘yan jarida da su tabbatar da tantance labarai kafin su watsa su, domin tabbatar da sahihanci da ingancin aikin jarida.
Da yake ƙarin bayani, ya ce gwamnatin Abdullahi Sule ta kawo sauye-sauye masu amfani, musamman wajen inganta harkar haƙar ma’adinai a jihar.
Ya bayyana cewa Jihar Nasarawa ce ke kan gaba a Naieriya wajen samar da ma’adinan Lithium, wanda ke amfani ga ci gaban tattalin arziƙi.
A nasa jawabin, Shugaban ‘Yan Jarida na Jihar, Kwamared Isaac Ukpoju, ya bayyana cewa sun kai ziyarar ne domin taya sabon Sakataren Gwamnatin Jihar murna bisa naɗin da aka yi masa.
Ya ce naɗin da aka yi wa Labaran Shuaibu Magaji ya dace da shi, kuma ‘yan jarida ba su yi mamaki ba duba da irin tarihin ayyukansa.
Haka kuma, ya roƙi Sakataren Gwamnatin da ya haɗa su cikin harkokin yaɗa labarai na gwamnati, musamman a ɓangaren tallafa wa ayyukansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Jarida Nasarawa Sakataren gwamnati
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu
Yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Comoros Azali Assoumani, sun aika wa juna sakon taya murnar cika shekaru 50 da kulla alakar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu.
A cikin sakonsa, shugaba Xi Jinping ya nuna cewa, yana mayar da hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Comoros, kuma yana son hada hannu da shugaba Azali, da amfani da cikar alakar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu shekaru 50, a matsayin wata dama ta ciyar da dangantakarsu ta gargajiya gaba, da ma inganta tabbatar da nasarorin da aka cimma a yayin taron koli na Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC), da bunkasa dangantakar dake tsakanin Sin da Comoros bisa manyan tsare-tsare, da kuma kara taka rawar gani wajen gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta Sin da Afirka ta ko wane lokaci a sabon zamani.
A nasa bangaren, shugaba Azali ya bayyana cewa, bisa yanayin da duniya ke ciki na fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice, ra’ayin da shugaba Xi Jinping ya gabatar na girmama ikon mulkin kai da rashin tsoma baki cikin harkokin gidan kasa da kasa tare kuma da cimma nasara tare ta hanyar hadin kai, ya kara wa kasashe masu tasowa kwarin gwiwa, ciki har da kasar Comoros. Ya ce kasarsa na son yin kokari tare da kasar Sin bisa ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil-Adam, don karfafa samun dauwamamman ci gaba irin na hakuri da juna, da ba da gudummawa ga inganta hadin kai da ma samun wadata tare a tsakanin Afirka da Sin. (Bilkisu Xin)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA