Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi maraba da matakin da kasar Yemen ta dauka na haramtawa jiragen ruwan Isra’ila shiga tekun Bahar Maliya

Bayan sanarwar da kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen ta fitar na cewa za ta dawo da haramcin da ta yi wa jiragen ruwan Isra’ila na tsallakawa tekun Bahar Rum, Hamas ta fitar da sanarwa inda ta yi maraba da matakin.

ta bayyana wannan mataki a matsayin wanda ke nuna hakikanin matsayin al’ummar Yemen da gwamnatin kasar na goyon bayan gwagwarmayar al’ummar Falastinu.

Har ila yau kungiyar ta yi kira ga dukkanin kasashen Larabawa da na Musulunci da kuma ‘yantatun kasashe a duniya da su kara zage damtse wajen matsin lamba ga ‘yan mamaya da magoya bayansu da su kawo karshen hare-haren wuce gona da iri kan Gaza, da dage shingen da aka yi musu, da kuma tabbatar da isar da kayayyakin jin kai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Wamban Shinkafi Ta Amince Da Tinubu a 2027

Jam’iyyar (APC) a ƙarƙashin kungiyar Wamban Shinkafi ta jihar Zamfara, ta bayyana goyon bayanta ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugabancin ƙasa guda ɗaya na jam’iyyar a zaben 2027.

Wannan sanarwar ta fito ne daga wanda ya kafa kungiyar kuma jigo a jam’iyyar APC a Zamfara, Dakta Sani Abdullahi Shinkafi, yayin taron masu ruwa da tsaki na kungiyar da aka gudanar a birnin Gusau, babban birnin jihar.

A cewar Shinkafi, amincewar da aka bayar ta biyo bayan wani motsi da Yushau Mada, kwamandan kungiyar, ya gabatar, wanda kuma Asma’u Gusau, shugabar mata ta amince da shi ta biyu.

Dakta Shinkafi ya ce, gwamnatin Najeriya a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu na tafiya kan turbar sauyi, ci gaba da gina ƙasa, tare da tabbatar da cewa yana da cikakken goyon bayansa ga jam’iyyar mai mulki. Ya kuma yi alkawarin ba da gudunmuwarsa wajen tabbatar da nasarar APC a dukkan matakai.

Ya bayyana cewa jam’iyyar APC a Zamfara ta kasance ɗaya mai haɗin kai, inda ya gargadi mambobi su guji ayyukan da za su cutar da jam’iyyar kafin da lokacin zaɓe.

Ya sake jaddada kudirinsa na kare ka’idojin dimokuraɗiyya da kyakkyawan shugabanci, yana mai cewa jagorancin Shugaba Tinubu ya kawo ci gaba mai ma’ana da gyare-gyare a fannoni daban-daban na ƙasar.

Shinkafi ya kuma yi alkawarin ci gaba da goyon baya ga shugabancin jam’iyyar APC a matakin ƙasa da jiha ƙarƙashin Tukur Danfulani, tare da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin mambobi.

Wannan amincewar da kungiyar Wamban Shinkafi Democratic Front ta bayar ga Shugaba Tinubu, na zuwa ne kwanaki goma bayan sashen jam’iyyar APC na Jihar Zamfara ya yi irin wannan sanarwa.

AMINU DALHATU/Gusau

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Kungiyar Wamban Shinkafi Ta Amince Da Tinubu a 2027
  • UNICEF ta ce Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza
  • Hamas ta soki kudurin Isra’ila na yin dokar hukuncin kisa kan laifin ta’addanci
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU
  • Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa
  •  Babu Wani Zabi Da Ya Rage Face Amincewa Da Iran A Matsayin Cibiyar Kimiyyar Masana’antar Nukiliya
  • Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5
  • Gwamnan Darfur: Babu zaman lafiya da masu yi wa al’ummar Sudan kisan gilla