Hamas ta yi maraba da matakin Yemen na haramtawa jiragen ruwan Isra’ila shiga teku
Published: 13th, March 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi maraba da matakin da kasar Yemen ta dauka na haramtawa jiragen ruwan Isra’ila shiga tekun Bahar Maliya
Bayan sanarwar da kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen ta fitar na cewa za ta dawo da haramcin da ta yi wa jiragen ruwan Isra’ila na tsallakawa tekun Bahar Rum, Hamas ta fitar da sanarwa inda ta yi maraba da matakin.
ta bayyana wannan mataki a matsayin wanda ke nuna hakikanin matsayin al’ummar Yemen da gwamnatin kasar na goyon bayan gwagwarmayar al’ummar Falastinu.
Har ila yau kungiyar ta yi kira ga dukkanin kasashen Larabawa da na Musulunci da kuma ‘yantatun kasashe a duniya da su kara zage damtse wajen matsin lamba ga ‘yan mamaya da magoya bayansu da su kawo karshen hare-haren wuce gona da iri kan Gaza, da dage shingen da aka yi musu, da kuma tabbatar da isar da kayayyakin jin kai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Wamban Shinkafi Ta Amince Da Tinubu a 2027
Jam’iyyar (APC) a ƙarƙashin kungiyar Wamban Shinkafi ta jihar Zamfara, ta bayyana goyon bayanta ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugabancin ƙasa guda ɗaya na jam’iyyar a zaben 2027.
Wannan sanarwar ta fito ne daga wanda ya kafa kungiyar kuma jigo a jam’iyyar APC a Zamfara, Dakta Sani Abdullahi Shinkafi, yayin taron masu ruwa da tsaki na kungiyar da aka gudanar a birnin Gusau, babban birnin jihar.
A cewar Shinkafi, amincewar da aka bayar ta biyo bayan wani motsi da Yushau Mada, kwamandan kungiyar, ya gabatar, wanda kuma Asma’u Gusau, shugabar mata ta amince da shi ta biyu.
Dakta Shinkafi ya ce, gwamnatin Najeriya a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu na tafiya kan turbar sauyi, ci gaba da gina ƙasa, tare da tabbatar da cewa yana da cikakken goyon bayansa ga jam’iyyar mai mulki. Ya kuma yi alkawarin ba da gudunmuwarsa wajen tabbatar da nasarar APC a dukkan matakai.
Ya bayyana cewa jam’iyyar APC a Zamfara ta kasance ɗaya mai haɗin kai, inda ya gargadi mambobi su guji ayyukan da za su cutar da jam’iyyar kafin da lokacin zaɓe.
Ya sake jaddada kudirinsa na kare ka’idojin dimokuraɗiyya da kyakkyawan shugabanci, yana mai cewa jagorancin Shugaba Tinubu ya kawo ci gaba mai ma’ana da gyare-gyare a fannoni daban-daban na ƙasar.
Shinkafi ya kuma yi alkawarin ci gaba da goyon baya ga shugabancin jam’iyyar APC a matakin ƙasa da jiha ƙarƙashin Tukur Danfulani, tare da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin mambobi.
Wannan amincewar da kungiyar Wamban Shinkafi Democratic Front ta bayar ga Shugaba Tinubu, na zuwa ne kwanaki goma bayan sashen jam’iyyar APC na Jihar Zamfara ya yi irin wannan sanarwa.
AMINU DALHATU/Gusau