Hamas ta yi maraba da matakin Yemen na haramtawa jiragen ruwan Isra’ila shiga teku
Published: 13th, March 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi maraba da matakin da kasar Yemen ta dauka na haramtawa jiragen ruwan Isra’ila shiga tekun Bahar Maliya
Bayan sanarwar da kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen ta fitar na cewa za ta dawo da haramcin da ta yi wa jiragen ruwan Isra’ila na tsallakawa tekun Bahar Rum, Hamas ta fitar da sanarwa inda ta yi maraba da matakin.
ta bayyana wannan mataki a matsayin wanda ke nuna hakikanin matsayin al’ummar Yemen da gwamnatin kasar na goyon bayan gwagwarmayar al’ummar Falastinu.
Har ila yau kungiyar ta yi kira ga dukkanin kasashen Larabawa da na Musulunci da kuma ‘yantatun kasashe a duniya da su kara zage damtse wajen matsin lamba ga ‘yan mamaya da magoya bayansu da su kawo karshen hare-haren wuce gona da iri kan Gaza, da dage shingen da aka yi musu, da kuma tabbatar da isar da kayayyakin jin kai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda
Kwamandan sojan kasar Pakitsan Asim Munir ya ce; Dole ne Taliban ta zabi wanda za ta yi mu’amala da hulda da su, ko dai gwamnatin Pakistan din, ko kuma ‘yan ta’adda.
Asim Munir wanda a makon da ya shude aka sake tabbatar da shi akan mukaminsa na shugaban sojojin kasar, ya kara da cewa sun isar da wannan sakon zuwa ga gwamnatin Taliban ta Afghanistan.
Haka nan kuma ya ce; Pakistan kasa ce mai son zaman lafiya,amma kuma a lokaci daya ba a shirye take ba, ta bari a tsokane ta akan abinda ta shafi zaman lafiya da kare hurumin kasarta.
A gefe daya, Asim Munir ya kuma gargadi makwabtansu na gabas, wato India yana mai cewa s fito daga cikin rudani, domin anan gaba idan wani abu ya faru, to martanin da Pakistan za ta mayar zai zama cikin sauri kuma da tsanani fiye da baya.
Ministan tsaron na Pakistan ya kuma ce, sojojin kasar sun sami gagarumin ci gaba wajen bunkasa ayyukansu, da kara zama cikin shiri, da kuma hanyoyin aiki tare a tsakanin dukkanin bangarorin tsaro.
A cikin watannin bayan nan dai an sami rashin jituwa a tsakanin kasashen Pakitsan da Afghanistan wanda ya kai ga musayar wuta na kwanani masu yawa. Kasashen Turkiya da Katar ne su ka shiga tsakani da ya kai ga tsagaita wutar yaki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci