Shugaban Kwamitin Tallafa wa Marayu na Riyadissalihin Funtua, Alhaji Lawal Mekaji (Madugun Kasuwar Funtua), ya yi kira ga al’umma, musamman iyaye da masu hannu da shuni, da su bada gudunmawa wajen tallafa wa marayu da inganta rayuwarsu.

Ya yi wannan kira ne yayin da yake raba kayan sutura da abinci ga marayu a Funtua a wani bangare na kokarinsa na yada albarkar watan Ramadan.

A cewarsa, kula da marayu ba kawai nauyin zamantakewa ba ne, amma wata gagarumar ibada ce da ke karfafa kyawawan dabi’u a cikin al’umma.

Da yake jawabi yayin taron rabon kayan, sakataren gidauniyar, Bashir Muhammad King, ya bukaci wadanda suka amfana da kayayyakin da su yi amfani da su ta hanyoyin da suka dace.

Ya kuma mika godiya ga duk wadanda suka bayar da gudunmawa domin nasarar shirin, yana mai jaddada cewa irin wannan karamci yana da matukar tasiri wajen kawo fata da sauki ga rayuwar mabukata.

Taron rabon kayan ya kasance mai cike da farin ciki da godiya daga marayu da masu kula da su, wanda hakan ya kara nuna muhimmancin hadin kan al’umma wajen daga darajar rayuwar marayu da marasa galihu.

COV/Magaji Yakawada

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gidauniya Kayayyaki Marayu Rabo Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce

Zuwa karfe 5:41 na daren ranar 7 ga watan Disamba, fim din Amurka “Zootopia 2” wanda aka fara nuna wa kwanaki 12 da suka wuce (tun daga ranar 26 ga Nuwamba), ya samu kudaden shiga a cikin kasar Sin da yawansa ya wuce yuan biliyan 30 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 424.8, adadin da ya zarce kudaden shiga da ya samu a kasashen Arewacin Amurka, har ya sa kasar Sin ta zama kasa mafi taka rawa wajen samar da kudin shiga ga wannan fim a duniya. Hakan kuma ya nuna yadda Sin ke da babbar kasuwar fina-finai.

Ibrahim Akopari Ahmed, jami’in kula da harkokin cinikayya a Najeriya, a zantawarsa da dan jarida a baya, ya taba bayyana cewa, “Najeriya na daya daga cikin manyan kasashe mafiya karfin tattalin arziki a Afirka, kuma sana’o’i masu alaka da samar da hidimomi ne ke ba da gudunmawa mafi yawa ga GDPn kasar, wanda ya zarce kashi 50 cikin 100 na GDP. Saboda haka, Najeriya tana da karfi a bangaren sana’o’in samar da hidimomi, musamman a fagen nishadantarwa, kamar masana’antun samar da fina-finai ta Najeriya (Nollywood). A wannan fage, muna kan gaba a Afirka.”

Najeriya babbar kasa ce ta samar da fina-finai a Afirka, yayin da Sin ke da babbar kasuwar kallon fina-finai. Hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu ta fannin fina-finai yana da makoma mai haske, kuma a hakika Sin da Najeriya na karfafa hadin gwiwa a wannan fanni. Alal misali, an gudanar da bikin fina-finai na kasa da kasa na Zuma karo na 15 a farkon wannan watan a babban birnin Najeriya Abuja, inda aka nuna fina-finai biyu daga Sin: wato “Rooting” da “Shen Zhou 13”. Babban manajan kamfanin samar da fina-finai ta Najeriya Ali Nuhu ya bayyana cewa, yana fatan ta wannan taron, za a kara zurfafa hadin gwiwar sana’o’in samar da fina-finai tsakanin Sin da Najeriya. Muna fatan a karkashin tsarin “dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka” da ma sauran irin dandalin hadin gwiwa, Sin da Najeriya za su kara karfafa huldar al’adunsu, ta yadda a nan gaba za a samu karuwar shigowar kyawawan fina-finai daga Najeriya zuwa nan kasar Sin, don baiwa masu kallo na kasar Sin karin damammaki na fahimtar Afirka, musamman Najeriya.(Mai zane da rubutu: MINA)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Ya Kamata Amurka Ta Daina Sa Hannu Cikin Harkokin Najeriya December 4, 2025 Ra'ayi Riga Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi December 4, 2025 Ra'ayi Riga Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu November 29, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • ‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026