Shugaban Kwamitin Tallafa wa Marayu na Riyadissalihin Funtua, Alhaji Lawal Mekaji (Madugun Kasuwar Funtua), ya yi kira ga al’umma, musamman iyaye da masu hannu da shuni, da su bada gudunmawa wajen tallafa wa marayu da inganta rayuwarsu.

Ya yi wannan kira ne yayin da yake raba kayan sutura da abinci ga marayu a Funtua a wani bangare na kokarinsa na yada albarkar watan Ramadan.

A cewarsa, kula da marayu ba kawai nauyin zamantakewa ba ne, amma wata gagarumar ibada ce da ke karfafa kyawawan dabi’u a cikin al’umma.

Da yake jawabi yayin taron rabon kayan, sakataren gidauniyar, Bashir Muhammad King, ya bukaci wadanda suka amfana da kayayyakin da su yi amfani da su ta hanyoyin da suka dace.

Ya kuma mika godiya ga duk wadanda suka bayar da gudunmawa domin nasarar shirin, yana mai jaddada cewa irin wannan karamci yana da matukar tasiri wajen kawo fata da sauki ga rayuwar mabukata.

Taron rabon kayan ya kasance mai cike da farin ciki da godiya daga marayu da masu kula da su, wanda hakan ya kara nuna muhimmancin hadin kan al’umma wajen daga darajar rayuwar marayu da marasa galihu.

COV/Magaji Yakawada

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gidauniya Kayayyaki Marayu Rabo Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Nigeria: Har Yanzu Da Akwai Daliban Makaranta 250 Da Suke Hannun Masu Garkuwa Da Su

Makwanni biyu bayan da masu garkuwa su ka sace kananan yara ‘yan mamaranta an bayyana cewa;har yanzu da akwai 250 a hannun barayin mutanen.

A ranar 21 ga watan Nuwamba ne dai masu dauke da makamai su ka kutsa cikin wata makaranta ta majami’ar Roman Katolika, su ka yi awon gaba da dalibai 300 da kuma malamai.

Mahukuntan makarantar sun ce dalibai 50 sun iya tserewa daga hannun wadanda su ka yi garkuwar da su, don haka har yanzu da akwai wasu 250 da suke a hannun barayin.

Sace daliban da aka yi na bayan nan, shi ne mafi muni,tun wanda aka yi wa daliban makarantar Chibok a 2014 da adadinsu ya kai 276 a hannun Bokoharam.

Jami’an tsaron kasar ta Najeriya sun ce ana ci gaba da kai gwauro da mari domin ganin an ‘yanto da daliban dake hannun barayin, sai dai iyayen yaran suna ci gaba da zama cikin damuwa a zullumi.

Satar mutane domin samun kudin fansa, ya zama ruwan dare a kasar Najeriya,musamman a arewacinta, inda barayin daji suke kama mutane da zummar samun kudin fansa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye December 6, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda December 6, 2025 Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa December 6, 2025 Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Trump Ya Yabawa Rwanda Da Kongo DMK Kan Sulhuntawa A Yakin Gabancin Kongo December 5, 2025 Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu December 5, 2025 Shin Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump? December 5, 2025 Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Nigeria: Har Yanzu Da Akwai Daliban Makaranta 250 Da Suke Hannun Masu Garkuwa Da Su
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi
  • Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi