Shugaban Kwamitin Tallafa wa Marayu na Riyadissalihin Funtua, Alhaji Lawal Mekaji (Madugun Kasuwar Funtua), ya yi kira ga al’umma, musamman iyaye da masu hannu da shuni, da su bada gudunmawa wajen tallafa wa marayu da inganta rayuwarsu.

Ya yi wannan kira ne yayin da yake raba kayan sutura da abinci ga marayu a Funtua a wani bangare na kokarinsa na yada albarkar watan Ramadan.

A cewarsa, kula da marayu ba kawai nauyin zamantakewa ba ne, amma wata gagarumar ibada ce da ke karfafa kyawawan dabi’u a cikin al’umma.

Da yake jawabi yayin taron rabon kayan, sakataren gidauniyar, Bashir Muhammad King, ya bukaci wadanda suka amfana da kayayyakin da su yi amfani da su ta hanyoyin da suka dace.

Ya kuma mika godiya ga duk wadanda suka bayar da gudunmawa domin nasarar shirin, yana mai jaddada cewa irin wannan karamci yana da matukar tasiri wajen kawo fata da sauki ga rayuwar mabukata.

Taron rabon kayan ya kasance mai cike da farin ciki da godiya daga marayu da masu kula da su, wanda hakan ya kara nuna muhimmancin hadin kan al’umma wajen daga darajar rayuwar marayu da marasa galihu.

COV/Magaji Yakawada

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gidauniya Kayayyaki Marayu Rabo Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.

 

 

A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.

 

Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.

 

Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.

 

Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.

 

Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fitar Da Nama Zuwa Saudiyya: Mayankar Dabbobi Ta Jurassic Ta Yi Hadin-gwiwa Da Shirin CDI
  • Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya
  • Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya
  • Hamas Ta Yi Gargadin Bullar Yunwa A Gaza A Cikin Watan Ramadan
  • Masu Goyon Bayan Falasdinu Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Don Bukatar Sakin Mahmoud Khalil A Tsakiyar Birnin New York
  • Kano: Gobara ta kashe mutum 7 da lalata kadarorin N50m a Fabrairu
  • Za a mayar da waɗanda Lakurawa suka raba da garuruwansu – Gwamnan Kebbi
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Rukuni Na Farko Na Masu Tsaron Makarantu
  • Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina