Aminiya:
2025-11-23@05:36:38 GMT

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya

Published: 11th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da ɗaukar salo iri-iri yayin da ’yan kasa da dama suka yi kasaƙe suna jiran girgiza ta gaba wadda wasu suke ganin tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya ɗiga mata ɗanba.

A baya-bayan nan dai an yi ta tsegunguma da rade-radi a kana bin da wasu jiga-jigan ’yan siyasar ƙasar nan, musamman ’yan adawa da ’ya’yan jam’iyya mai mulki waɗanda suke takun saƙa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suke ƙullawa

Yanzu ta fara wari, an ji Malam Nasiru ya bayar da sanarwar ficewarsa daga jam’iyyar APC da tsallakawa zuwa SDP.

NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana

Shin ko me zai biyo bayan wannan girgiza da tsallen baɗaken Malam Nasiru da dirarsa suka haifar?

Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai duba.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Siyasar Nijeriya Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar tsaro a Arewa na damuna matuƙa — Tinubu

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce matsalar tsaro a yankin Arewa na damunsa matuƙa saboda tana kawo cikas ga zaman lafiya da ci gaban Najeriya.

Ya bayyana haka ne a Jihar Kaduna, yayin bikin cikar Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), wanda Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya wakilce shi.

’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin Najeriya

Tinubu, ya ce gwamnatinsa ta gaji matsalolin tsaro masu yawan gaske, amma tana aiki tuƙuru don magance su.

Ya yi gargaɗin cewa Najeriya ba za ta ci gaba ba idan al’ummarta suka ci gaba da fuskantar hare-hare, talauci, da tsoro.

“Ba abin da ke damuna kamar matsalar tsaro a Najeriya, musamman a Arewa. Ba za mu ci gaba ba idan wani yanki yana cikin matsala.”

Ya yi kira ga shugabannin Arewa da su zama masu gaskiya da jarumta wajen nemo mafita.

Ya kuma yi alƙawarin cewa gwamnatinsa za ta kawo ƙarshen ’yan ta’adda da ’yan fashi, tare da farfaɗo da tattalin arziƙin yankin.

“Mun gaza daga ranar da muka yi bacci lafiya alhali miliyoyin jama’a suna kwana cikin yunwa, matafiya suna tsoron yin tafiya.”

Tinubu ya ce yana fatan ganin Arewa mai aminci, ciki har da samar da man fetur daga yankunan Arewa da manyan ayyuka kamar sabon titin Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano.

Shugaban kwamitin amintattu na ACF, Alhaji Bashir Dalhatu, ya yi Allah-wadai da kashe-kashe da garkuwa da ɗalibai da malamai a jihohin Neja da Kebbi.

Ya roƙi gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa don kawo ƙarshen tashin hankali.

“Kashe-kashe, sace ɗalibai, da hare-haren da ake kai wa jami’an tsaro ba za su ci gaba da aukuwa ba. Gwamnati dole ta nemo hanyar kawo ƙarshen wannan lamari.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar tsaro a Arewa na damuna matuƙa — Tinubu
  • Rundunar Sojan Iran Tana Cikin Shirin Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana
  • Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Iran Ta yi Gargadi Game Da Sakamakon Da  Zai Iya Faruwa A Yankin Bayan Shigar Isra’ila Kasar Siriya
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia
  • NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki