Aminiya:
2025-06-30@22:04:10 GMT

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya

Published: 11th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da ɗaukar salo iri-iri yayin da ’yan kasa da dama suka yi kasaƙe suna jiran girgiza ta gaba wadda wasu suke ganin tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya ɗiga mata ɗanba.

A baya-bayan nan dai an yi ta tsegunguma da rade-radi a kana bin da wasu jiga-jigan ’yan siyasar ƙasar nan, musamman ’yan adawa da ’ya’yan jam’iyya mai mulki waɗanda suke takun saƙa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suke ƙullawa

Yanzu ta fara wari, an ji Malam Nasiru ya bayar da sanarwar ficewarsa daga jam’iyyar APC da tsallakawa zuwa SDP.

NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana

Shin ko me zai biyo bayan wannan girgiza da tsallen baɗaken Malam Nasiru da dirarsa suka haifar?

Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai duba.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Siyasar Nijeriya Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Yunwa ta kashe ƙananan yara 66 a Gaza

Hukumomi sun tabbatar da mutuwar ƙananan yara 66 a sakamakon yunwa a yankin Gaza.

Yaran sun mutu a yayin da sojojin Isra’ila ke ci gaba da hana shigar da madarar yara da sauran kayan abinci da sauran kayan jinƙai da ake buƙata domin ceto rayuka zuwa Gaza.

Mutuwar yaran ta zo ne a daidai lokacin da hukumomin Gaza suka sanar cewa sojojin Isra’ila sun kashe wasu Palasdinawa 34.

Jami’an lafiya a Asibitin Al-Shifa da ke Gaza sun bayyana cewa an kawo gawarwakin wasu mutum 12 da sojojin Isra’ila suka kashe a filin wasa da Palasdinawa ke zaman mafaka, da wasu takwas da aka kashe a wani gida.

‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’ Yadda aka yi jana’izar kwamandojin Iran da Isra’ila ta kashe

Ofishin yaɗa labarai na hukumomin Gaza ya bayyana cewa ana matuƙar buƙatar kayan abincin domin ceto rayuwar musamman ƙananan yara da gajiyayyu da marasa lafiya.

Sanarwar Hukumar ta ce, “laifin yaƙi ne da tauye haƙƙin ɗan Adam ne abin da Isra’ila ke yi na amfani da salon hana faren hula samun abinci a matsayin makami.

“Wannan ya saɓa da yarjejeniyar Geneva da kuma dokokin ayyukan jinƙai na duniya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sanya dokar hana fita a Kaduna
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  • Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya
  • Tarihi da tasirin rayuwar Alhaji Aminu Alhassan Dantata
  • Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa
  • Yunwa ta kashe ƙananan yara 66 a Gaza
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe