NNPC Da Dangote Na Shirin Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Kan Sayen Ɗanyen Mai
Published: 11th, March 2025 GMT
Masana na gargaɗin cewa idan NNPC ta daina sayar wa matatar Dangote mai a naira, hakan na iya haifar da hauhawar farashin man fetur, maimakon rage farashin da ake tsammani.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
Kano Ta Kaddamar da Kwamitin Jagoranci Don Shirin Tarayyar Turai na Ilimi da Ƙarfafa Matasa
Daga Khadijah Aliyu
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da Kwamitin Jagorancin Shirin Ilimi da Ƙarfafa Matasa a Arewa maso Yammacin Najeriya (EYEPINN) wanda kungiyar Tarayyar Turai ke daukar nauyinsa domin fadada damar samun ingantaccen ilimi da kuma karfafa gwiwar matasa a yankin.
An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Kano, karkashin jagorancin Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda.
Yayin jawabinsa, Dakta Makoda ya bayyana shirin EYEPINN a matsayin “Alƙawari mai Manufa”, yana mai cewa manufar shirin ita ce cike gibi a fannin ilimi, karfafa haɗin kai, da kuma baiwa matasa kwarewar da ta dace domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a jihar.
Ya ce sabon kwamitin da aka kaddamar zai yi jagoranci kan dabaru, tsare-tsare, kulawa da tabbatar da gaskiya da inganci wajen aiwatar da ayyukan EYEPINN a fadin Kano.
Dakta Makoda ya kara da cewa, mambobin kwamitin sun haɗa da wakilai daga ma’aikatun gwamnati, hukumomi da cibiyoyi masu ruwa da tsaki, abokan hulɗa, da kuma wakilan Tarayyar Turai.
A yayin taron, abokan hulɗa ciki har da UNICEF, PLAN International, UNESCO, da kuma sashen nazari na ci gaban duniya (DIME) na Bankin Duniya, sun gabatar da jawabai da suka fayyace manufofi, da sakamakon da ake sa ran samu, da tsarin haɗin gwiwa, domin ƙarfafa tsarin samar da ilimi da kuma ƙarfafa matasa a Kano da ma yankin Arewa maso Yamma baki daya.