Aminiya:
2025-12-13@14:37:14 GMT

Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya miƙa wa majalisar dokokin jihar sunan Ibrahim Yakubu Adamu domin tantancewa da tabbatar da naɗinsa a matsayin sabon Kwamishina.

Kakakin Majalisar, Alhaji Jibrin Falgore ne ya bayyana hakan yayin da yake karanta wasiƙar gwamnan a zaman majalisar da ya gudana a yau Litinin.

Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC

Aminiya ta ruwaito cewa, Ibrahim Yakubu Adamu wanda gwamnan ke shirin naɗawa muƙamin kwamishina shi ne Shugaban Hukumar Tsara Birane ta Kano, KNUPDA.

Falgore ya ce nan gaba kaɗan za su aika masa goron gayyata domin tabbatar da buƙatar gwamnan.

Kazalika, majalisar ta kuma tabbatar da dokar kafa sabuwar Hukumar Kula da Gine-Ginen Gwamnati da Ababen More Rayuwa.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussein na jam’iyyar NNPP daga Ƙaramar Hukumar Dala, ya ce sabuwar hukumar ce za ta riƙa ɗawainiyar kula da gine-ginen gwamnati da sauran ababen more rayuwa da suka haɗa da tituna, gadoji da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ibrahim Yakubu Adamu Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA

Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 26 ga Fabrairu, 2026 domin yanke hukunci a shari’ar da Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) ta shigar kan DCP Abba Kyari, wanda aka dakatar.

NDLEA na tuhumar Abba Kyari, tsohon Shugaban Rundunar ’Yan Sanda Masu Yaƙi da Garkuwa d a Mutane (IRT), tare da ’yan uwansa biyu kan zargin rashin bayyana kadarorinsu.

A ranar Juma’a Mai shari’a James Omotosho ya sanya ranar, bayan lauyoyin NDLEA, Sunday Joseph; lauyan Abba Kyari, Onyechi Ikpeazu, SAN; da lauyan ’yan uwansa, Monjok Agom, sun gabatar da hujjoji da muhawara kan tuhumar.

A cikin tuhumar da ta ƙunshi laifuffuka 23, NDLEA ta ce ta gano kadarori 14, ciki har da manyan shaguna, gidaje, filin wasan polo, filaye da gonaki mallakar Abba Kyari, a Babban Birnin Tarayya Abuja da Maiduguri a Jihar Borno.

Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699

NDLEA ta kara da cewa ta gano sama da Naira miliyan 207 miliyan da kuma Yuro 17,598 a asusun bankunan Abba Kyari daban-daban, ciki har da Guarantee Trust Bank, United Bank for Africa da Sterling Bank.

Hukumar ta kuma zargi waɗanda ake tuhuma su da ɓoye mallakar kadarori da kuma juya kuɗaɗen.

NDLEA ta ce yin hakan laifuffuka ne a ƙarƙashin Dokar NDLEA da kuma Dokar Hana Safarar Kuɗaɗe.
Sai dai wadanda ake tuhuma sun ce ba su amince da dukkan tuhumar ba.

NDLEA ta kira shaidu 10 domin tabbatar da tuhumar, tare da gabatar da aƙalla hujjoji 20.
Duk da haka, Abba Kyari, ya gabatar da buƙatar a watsar da shari’ar bayan masu gabatar da bayanansu.

Abba Kyari, ta bakin lauyansa, ya ce masu gabatar da ƙara sun kasa kawo hujja da ke nuna shi ne mai mallakar kadarorin da ake zargi.

Amma a ranar 28 ga Oktoba, Mai shari’a Omotosho ya yi watsi da bukatarsa, inda ya ce masu gabatar da kara sun kafa hujja ta farko da ke buƙatar wadanda ake tuhuma su kare kansu.

Kyari, ya dage cewa ya bayyana kadarorinsa da na matarsa bisa ƙa’ida, ya kuma musanta mallakar wasu kadarorin da NDLEA ta danganta masa, inda ya bayyana cewa wasu daga cikin kadarorin na mahaifinsa ne da ya rasu, wanda ya bar ’ya’ya kusan 30.

Ya kuma ƙaryata zargin mallakar filin wasan polo a Borno, inda ya ce abin mamaki ne a danganta masa wannan katafaren fili.

A ranar 26 ga Nuwamba, 2025, Abba Kyari ya rufe kare kansa bayan ya gabatar da hujjoji ta bakin lauyansa, kuma aka yi masa tambayoyi daga lauyan NDLEA.

Sai dai ‘yan uwansa biyu (Mohammed da Ali), ta bakin lauyansu Monjok Agom, sun shaida wa kotu cewa ba za su kira wani shaida ba, inda suka ce za su jingina shari’arsu da hujjojin masu gabatar da ƙara.

Wannan shari’ar ta daban ce da ta zargin safarar hodar iblis da yake fuskanta tare da wasu ‘yan sanda a gaban Mai shari’a Emeka Nwite na wata Babban Kotun Tarayya da ke Abuja.

Dukkan shari’o’in biyu, NDLEA ce ta shigar da su a shekarar 2022

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farfesa na Farko a fannin Ilimi a Arewa, Adamu Baikie, ya rasu yana da shekara 94
  • Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Kiyasta Naira Biliyan 3 Don Ayyukan Hajjin 2026
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a