Aminiya:
2025-04-30@23:15:27 GMT

Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya miƙa wa majalisar dokokin jihar sunan Ibrahim Yakubu Adamu domin tantancewa da tabbatar da naɗinsa a matsayin sabon Kwamishina.

Kakakin Majalisar, Alhaji Jibrin Falgore ne ya bayyana hakan yayin da yake karanta wasiƙar gwamnan a zaman majalisar da ya gudana a yau Litinin.

Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC

Aminiya ta ruwaito cewa, Ibrahim Yakubu Adamu wanda gwamnan ke shirin naɗawa muƙamin kwamishina shi ne Shugaban Hukumar Tsara Birane ta Kano, KNUPDA.

Falgore ya ce nan gaba kaɗan za su aika masa goron gayyata domin tabbatar da buƙatar gwamnan.

Kazalika, majalisar ta kuma tabbatar da dokar kafa sabuwar Hukumar Kula da Gine-Ginen Gwamnati da Ababen More Rayuwa.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussein na jam’iyyar NNPP daga Ƙaramar Hukumar Dala, ya ce sabuwar hukumar ce za ta riƙa ɗawainiyar kula da gine-ginen gwamnati da sauran ababen more rayuwa da suka haɗa da tituna, gadoji da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ibrahim Yakubu Adamu Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar

Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa  da ita ba.

 A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an  gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.”

Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”

Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.

Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.

A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar