Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano
Published: 10th, March 2025 GMT
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya miƙa wa majalisar dokokin jihar sunan Ibrahim Yakubu Adamu domin tantancewa da tabbatar da naɗinsa a matsayin sabon Kwamishina.
Kakakin Majalisar, Alhaji Jibrin Falgore ne ya bayyana hakan yayin da yake karanta wasiƙar gwamnan a zaman majalisar da ya gudana a yau Litinin.
Aminiya ta ruwaito cewa, Ibrahim Yakubu Adamu wanda gwamnan ke shirin naɗawa muƙamin kwamishina shi ne Shugaban Hukumar Tsara Birane ta Kano, KNUPDA.
Falgore ya ce nan gaba kaɗan za su aika masa goron gayyata domin tabbatar da buƙatar gwamnan.
Kazalika, majalisar ta kuma tabbatar da dokar kafa sabuwar Hukumar Kula da Gine-Ginen Gwamnati da Ababen More Rayuwa.
Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussein na jam’iyyar NNPP daga Ƙaramar Hukumar Dala, ya ce sabuwar hukumar ce za ta riƙa ɗawainiyar kula da gine-ginen gwamnati da sauran ababen more rayuwa da suka haɗa da tituna, gadoji da sauransu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ibrahim Yakubu Adamu Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
Kungiyar ‘Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya’ ta yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan Iran
Kasashe mambobin kungiyar aminan yarjejeniyoyin Majalisar Dinkin Duniya sun fitar da wata sanarwa ta musamman inda suka yi kakkausar suka kan wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Sanarwar ta yi la’akari da harin hadin gwiwa ta sama da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar a ranar 13 ga watan Yuni a kan wasu wurare da dama a Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkata wasu daruruwa da suka hada da mata da kananan yara da masana kimiyya, matakin da ya saba wa Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
‘Yan kungiyar sun kuma yi Allah wadai da harin ganganci kan fararen hula, da wuraren zaman jama’a, da kuma cibiyoyin nukiliyar na zaman lafiya, suna masu gargadin cewa irin wadannan ayyuka na iya haifar da watsuwar kayan aikin kimiyya da zai zama babbar barazana ga rayuwar fararen hula da muhalli.
Kungiyar ta yi kira da a tsaya tsayin daka kan amfani da karfi a kan Iran, tana mai jaddada nauyin da ke wuyan babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na kiyaye manufofi da ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar.
Har ila yau, ta jaddada aikin babban daraktan hukumar ta IAEA na yin Allah wadai da hare-haren da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kaiwa kan cibiyoyin nukiliyar Iran.