Shugaban karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Aliyu, ya tabbatar da harin da ‘yan ta’addan Lakurawa suka kai a yankin, inda suka kashe mutane kimanin 15 tare da kona kauyuka 7.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga gidan rediyon Najeriya da ke jihar Kebbi, shugaban karamar hukumar ya ce an baza jami’an tsaro a yankin domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

A cewar wata majiya mai tushe, Malam Umar, maharan sun kara kona akalla wasu kauyuka bakwai da ke kusa da Birnin Dede, duk a cikin karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbin.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Malam Umar ya bayyana cewa, an kai harin ne domin ramuwar gayya kan kisan da jami’an tsaro suka yi wa shugaban nasu a makon da ya gabata, inda ya kara da cewa, maharan sun bar kauye daya ne kawai, wanda sojoji ke gadinsa.

“Harin na daren Lahadin da ta gabata tamkar ramuwar gayya ne biyo bayan kashe shugaban Lakurawa, Maigemu da hadin gwiwar jami’an tsaro suka yi a Kebbi”. 

Sai dai Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kebbi, SP Nafiu Abubakar, bai amsa kiran waya ko sakon waya da ake neman karin bayani kan lamarin ba.

 

Daga Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lakurawa

এছাড়াও পড়ুন:

 Sojojin Sudan Sun Kwace Wuri Na Karshe Da Yake A Hannun “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” A Cikin Birnin Khartum

Rundunar sojan Sudan ta sanar da shimfida ikonta akan filin saukar jiragen sama na Khartum wanda shi ne tunga ta karshe da ta saura a hannun rundunar kai daukin gaggawa.

Kwamandan rundunar sojan Sudan da take fada a birnin na Khartum Lafatnar kasar Abdurrahman al-Bilawi ne ya sanar da cewa, an  shimfida iko a  cikn filin saukar jiragen sama na kasa da kasa na birnin Khartum.

Har ila yau yau kwamandan sojan ya kuma bayyana cewa, a yanzu haka suna cigaba da faraurar mayakin “Rundunar Kai Daukin Gaggawa”da su ka saura a cikin binin Khartum.

Tun da safiyar yau Laraba ne dai sojojin na Sudan suka sanar da cewa suna samun Karin nasara akan abokan fadansu.

Wata majiyar ta shaida wa kamfanin dillancin labaurn Faransa cewa; sojojin Sudan din sun killace  yankin Jabalu-Auliya, dake kudancin Khartum, da kuma hanyoyin da su ka nufi kusurwowin arewa, kudu da gabas.

Kwanaki kadan da su ka gabata ne dai sojojin na Sudan su ka kwato fadar shugaban kasa wacce ta dauki shekaru biyu a hannun rundunar kai daukin gaggawa, haka nan kuma babbar cibiyar soja da tsakiyar birnin Khartum da can ne ma’aikatu da dama suke.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ƙwato wa mutumin da aka sace kuɗin fansarsa a Kano
  • Sallah: ’Yansanda Sun Yi Alƙawarin Tabbatar Da Tsaro A Kano
  • Zamu Tabbatar Ingantuwar Depon Sojoji Na Zaria – Ministan Tsaro Badaru
  • Lakurawa sun kashe jami’an Kwastam 2 a Kebbi
  • Sudan : Janar al-Burhan Ya Shelanta ‘yantar Da Birnin Khartoum
  •  Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno
  •  Sojojin Sudan Sun Kwace Wuri Na Karshe Da Yake A Hannun “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” A Cikin Birnin Khartum
  • Boko Haram Ta Kashe Sojoji A Wani Sabon Hari A Borno
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul