Manya-manyan Jiragen ruwan yaki na kasashen Rasha da China sun isa tashar Jeragen ruwa ta Chabahar dake kudu maso gabacin kasar Iran a bakin tekun india don fara atisayen soje a tsakanin kasashen uku, wanda aka sanyawa suna ‘damarar tsaro na shekara ta 2025.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa wannan gagarumin atisayen sojojin ruwa tsakanin manya-manyan kasashen guda uku zai sami halattan wasu kasashe da dama a matsayin masu kallo.

Labarin ya kara da cewa manya-manyan jami’an sojojin ruwa na sojojin Iran da kuma na dakarun IRGC ne suka tarbi jiragen ruwan yaki na wadannan kasashe. Sannan ana saran wakilai daga kasashen Azerbaijan, Iraki, Kazakhstan, Oman, Pakistan, Qatar, Afirka ta Kudu, Sri Lanka da Haddiyar daular Larabawa, za su halarci atisayen wanda za’a fara a gobe talata daga tashar jiragen ruwa ta chabahar don kallon yadda atisayen zai kasance.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

A yau Talata ne firaministan Sin Li Qiang, ya gana da kakakin majalisar wakilan tarayyar Najeriya Tajudeen Abbas, wanda ya isa birnin Shanghai don halartar baje kolin CIIE karo na takwas.

Yayin zantawarsu, Li Qiang ya bayyana aniyar kasar Sin ta karfafa salon wanzar da ci gaba bisa manyan tsare-tsare tare da Najeriya, da zage damtse wajen aiwatar da wasu muhimman matakai goma na bunkasa kawance tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, da hada hannu wajen gina shawarar “Zira Daya Da Hanya Daya” mai inganci, da bunkasa matakin hadin gwiwa a sassan gargajiya, da fadada hadin gwiwa a sabbin masana’antu, da kara kyautata gina tattalin arziki da zamantakewar al’ummun sassan biyu.

Li Qiang ya kara da cewa, akwai bukatar kasashen biyu su karfafa tsare-tsare, da hadin gwiwa a fannin gudanar da cudanyar mabambantan sassa, karkashin irinsu hadakar kasashen BRICS, da MDD, da yayata hadin kai, da inganta karfin kasashe masu tasowa.

A nasa tsokacin, Tajudeen Abbas ya ce Najeriya na rike da manufar nan ta Sin daya tak a duniya, kuma a shirye take ta karfafa musayar kwarewar jagoranci tare da Sin, da fadada hadin gwiwa a sassa da dama, kamar tattalin arziki da cinikayya, da samar da ababen more rayuwa, da makamashi, da al’adu, tare da ci gaba da daga cikakkiyar dangantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Najeriya da Sin zuwa babban matsayi. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa November 4, 2025 Daga Birnin Sin Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha November 4, 2025 Daga Birnin Sin Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin November 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Kwamitin Gwamnonin IAEA
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya
  • Hamas Ta yi Watsi Da Batun Tura Sojojin Kasashen Waje Zuwa Gaza
  • Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
  • Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha
  • “Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
  • Mutum Daya Ya Yi Shahada Sanadiyyar Harin Sojojin HKI A Kudancin Lebanon
  • ’Yan Sandan Legas sun ayyana neman Sowore ruwa a jallo