Gwamnatin Kano Ta Bullo Da Sabbin Hanyoyin Kare Makarantunta Daga Kalubalen Tsaro
Published: 10th, March 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya ce gwamnatinsa ta dauki wani muhimmin mataki na tabbatar da tsaron makarantunta, inda za a hada hannu da masu ruwa da tsaki don kara karfafa tsaro a yankunan da makarantu suke.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin bikin bude taron masu ruwa da tsaki kan harkar tsaro a jihar da kuma horas da jami’an tsaron makarantu, wanda aka gudanar a fadar gwamnatin jihar.
Gwamnan wanda kwamishinan Ilimi Alhaji Ali Haruna Makoda ya wakilta, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki kudirin gwamnatinsa na bunkasa fannin ilimi a jihar.
Ya ce yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar kalubale wajen tabbatar da tsaro a makarantu, wannan shirin wani muhimmin mataki ne na karfafa tsaro da inganta yanayin koyo.
A jawabinsa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abayomi Shogunle, ya jaddada muhimmancin tsaro a makarantun, inda ya bayyana cewa abu ne da gwamnati mai ci ta ba da fifikoa kai.
Ya yi nuni da cewa, Sifeto janarna ‘yan sanda ne ya kaddamar da rundunar tsaro ta makarantu da nufin magance matsalolin tsaro a makarantun firamare da sakandare da manyan makarantu.
Shi ma a nasa jawabin mataimakin shugaban jami’ar Aliko Dangote, Farfesa Musa Tukur Yakasai, ya yabawa horon kan inganta tsaro a cibiyoyin ilimi.
Tun da farko Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun, wanda mataimakin sufeto janar shiyya ta daya AIG Ahmad Ammani ya wakilta, ya jaddada muhimmancin hada hannu tsakanin jama’a da jami’an tsaro domin magance matsalar rashin tsaro a makarantu da cibiyoyi.
Taron mai taken “Karfafa Tsaro da Hadin Kan Al’umma wajen Kare Ilimi,” ya hada wakilai daga ‘Yan sandan Najeriya, da rundunar Soji, da cibiyoyin ilimi da dai sauransu.
Taron ya samu halartar shugabannin hukumomin tsaro na Kano da sauran masu ruwa da tsaki.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Makarantu Tsaro masu ruwa da tsaki tsaro a makarantu
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae, a karon farko da yayi magana dangane da fashewar tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae ya gabatar da Ta’ziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu ko suka jikata a wannan hatsarin. Ya kuma bukaci a gudanar da bincike mai mai zurfi don gano musabbabin fashewar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jagoran yana bada umurni ga ma’aikatar shari’aa a kasar ta gudanar da cikekken bincike don sanin abinda ya faru saboda daukar matakan da suka dace don hana irin wannan sake faruwa nan gaba, sannan idan akwai wadanda suka yi kuskure a hukunta su.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gobarar da ta taso a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajae, daya daga cikin tashoshin jirage masu muhimmanci a tattalin arzikin kasar, don haka dole ne a kara daukar matakan tsaro da amincin tashar don hana irin wannan sake faruwa.
Sanadiyyar wannan hatsarin majalisar dokokin kasar ta shelanta makoki a duk fadin kasar a yau Litinin. Sannan shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan ya ziyarci tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae don ganewa idanunsa abubuwan da suka faru da kuma barnan da aka tabka.
Ya zuwa yanzun wadanda suka rasa rayukansu sun kai 40 sannan wadanda suka rasa rayukansu sun kai dubu guda.