Aminiya:
2025-06-15@21:22:41 GMT

Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa

Published: 8th, March 2025 GMT

Majaliar Dattawa ta ce ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ne saboda saɓa dokokin majalisar da ta yi, ba don zargin cin zarafin da ta yi wa shugaban majalisar ba.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Bamidele Opeyemi ne bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a madadin majalisar.

Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano

A cewarsa, dakatar da Sanata Natasha, mataki ne da duka majalisar ta ɗauka, saboda saɓa dokokinta da ta yi kamar yadda kwamitin ɗa’a da ladabtarwa ya tabbatar.

“An dakatar da ita ne saboda yadda take keta dokoki da ƙa’dojin majalisa, da nuna rashin ɗa’a a majalisar, wannan shi ne laifinta babu daɗi babu ragi.”

Sanarwar ta ce da a ce Sanata Natasha ta yi aiki da dokoki da ƙa’idojin majalisar, da majalisar za ta karɓi ƙorafinta, kamar yadda doka ta tanada.

“Amma ba ta bi ƙa’ida da dokokin da suka kafa majalisar da take aiki a cikinta ba.”

Sanata Bamidele ya ce majalisar ta ɗauki matakin dakatar da Sanata Natasha ne bisa shawarar kwamitin ɗa’a, wanda ya same ta da laifin saɓa wa sashe na 6.1 da sashe na 6.2 na dokokin majalisar.

Sanarwar ta kuma zayyano wasu laifuka biyar da ta ce Sanata Natasha ta aikata, ciki har da ƙin zama a kujerar da aka sauya mata a lokacin zaman majalisar na ranar 25 ga watan Fabrairu, da yin magana ba tare da amincewar jagoran zaman majalisar ba, da yin kalaman zagi da rashin girmamawa da shugabancin majalisar.

Aminiya ta ruwaito cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce Majalisar Dattawan Najeriya ta dakatar da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti Uduaghan har na tsawon wattani shida a kan laifin saɓa wa dokokin majalisar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa dakatar da Sanata Natasha majalisar da a majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano

Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daba masa wuta.

Bayanai sun nuna cewa barayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.

BBC ya ruwaito mutumin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), Kwamared Bashir Muhammad, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje