Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa
Published: 8th, March 2025 GMT
Majaliar Dattawa ta ce ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ne saboda saɓa dokokin majalisar da ta yi, ba don zargin cin zarafin da ta yi wa shugaban majalisar ba.
Shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Bamidele Opeyemi ne bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a madadin majalisar.
A cewarsa, dakatar da Sanata Natasha, mataki ne da duka majalisar ta ɗauka, saboda saɓa dokokinta da ta yi kamar yadda kwamitin ɗa’a da ladabtarwa ya tabbatar.
“An dakatar da ita ne saboda yadda take keta dokoki da ƙa’dojin majalisa, da nuna rashin ɗa’a a majalisar, wannan shi ne laifinta babu daɗi babu ragi.”
Sanarwar ta ce da a ce Sanata Natasha ta yi aiki da dokoki da ƙa’idojin majalisar, da majalisar za ta karɓi ƙorafinta, kamar yadda doka ta tanada.
“Amma ba ta bi ƙa’ida da dokokin da suka kafa majalisar da take aiki a cikinta ba.”
Sanata Bamidele ya ce majalisar ta ɗauki matakin dakatar da Sanata Natasha ne bisa shawarar kwamitin ɗa’a, wanda ya same ta da laifin saɓa wa sashe na 6.1 da sashe na 6.2 na dokokin majalisar.
Sanarwar ta kuma zayyano wasu laifuka biyar da ta ce Sanata Natasha ta aikata, ciki har da ƙin zama a kujerar da aka sauya mata a lokacin zaman majalisar na ranar 25 ga watan Fabrairu, da yin magana ba tare da amincewar jagoran zaman majalisar ba, da yin kalaman zagi da rashin girmamawa da shugabancin majalisar.
Aminiya ta ruwaito cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce Majalisar Dattawan Najeriya ta dakatar da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti Uduaghan har na tsawon wattani shida a kan laifin saɓa wa dokokin majalisar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa dakatar da Sanata Natasha majalisar da a majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa
Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke Gashuwa (FUGA) a jihar Yobe za ta gwangwaje Uwargidan Shugaban Sasa, Sanata Remi Tinubu, da gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, da wasu fitattun ’yan Najeriya shida da digirin girmamawa.
A cewar jami’ar, za a ba su shaidar ce saboda gudunmawar da suka bayar a bangarori da daman a ci gaban kasa.
Mataimakiyar Shugabar Jami’ar, Farfesa Maimuna Waziri ce ta bayyana hakan a lokacin da take ganawa da manema labarai a jami’ar.
Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss MustaphaTa ce za a karrama su ne a yayin bikin yaye dalibai karo na farko na jami’ar da zai gudana ranar Asabar mai zuwa.
Farfesa Maimuna ta ce za a karrama Sanata Remi ne da digirin digirgir ne na (D.Litt), yayin da Gwamna Buni da Ministan harkokin ’Yan Sanda kuma tsohon gwamnan Yobe, Sanata Ibrahim Geidam, dukkansu za su samu digirin digirgir ne a kan kwarewa kan harkokin mulki (DPA).
Ta kuma ce za a karrama tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmed Lawan da digirin digirgir bangaren kimiyya na D.Sc.
Haka kuma a cikin wadanda za a karrama akwai Mai shari’a Sidi Bage Muhammad da kuma Alhaji Bukar Goni Aji.
Farfesa Waziri ta ce jami’ar ta yaye dalibai kusan sau shida wadanda adadinsu ya kai 3,449 a tsangayoyin jami’ar guda hudu tun bayan da aka kafa ta.