Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?
Published: 8th, March 2025 GMT
Rikicin ya fara ne tun bayan tsige Obasa a ranar 13 ga Janairu, 2025, a matsayin shugaban majalisar. ‘Yan majalisa 33 a zaman da aka yi a wannan rana suka tsige Obasa tare da ayyana tsohowar mataimakiyar shugaban majalisar, Merand a matsayin shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.
Ko da yake ’yan majalisar sun yi nuni da cewa yana cin zarafin mukami da karkatar da kudade da kuma rashin da’a a matsayin wani bangare na dalilan tsige Obasa, matakin ya nuna asalin rikicin da ya barke a majalisar ta 10 a jihar.
‘Yan majalisar dai sun tsige Obasa ne a lokacin da yake kasar Amurka.
Bayan dawowarsa Legas a ranar 25 ga Janairu, 2025, ya kalubalanci cire shi.
Duk da tsoma bakin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC, musamman tsofaffin gwamnonin jihohin Osun da Ogun, Cif Bisi Akande da Cif Olusegun Osoba, ba a warware rikicin shugabancin ba.
Ita ma majalisar ba da shawara kan harkokin mulki a jihar ta kasa shawo kan rikicin, inda wasu mambobin ke ganin cewa Shugaban kasa Bola Tinubu ne kadai zai iya shiga tsakani yadda ya kamata.
Sai dai duk da shiga tsakani da kwamitin sasantawa da Akande ya jagoranta da Tinubu ya shirya domin warware matsalar, da alama rikicin ya kara kamari. Kwamitin dai ya gana da ‘yan kungiyar GAC da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar da kuma ‘yan majalisar, duk da haka bai hakarsa ba ta cimma ruwa ba.
A ranar Alhamis da ta gabata ne Obasa, wanda bai halarci majalisar ba tun bayan tsige shi, ya koma harabar majalisar a wani mataki na ban mamaki.
Matakin dai ya sanya masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da sauran al’umma cikin kaduwa, yayin da sabon al’amarin ya kara jefa majalisar cikin rudani.
Duk da shigarsa ofishin, ‘yan majalisa 35 ne suka ki amincewa da Obasa, yayin da ‘yan majalisa hudu suka yi zaman da shi a wannan rana.
A zama na karshe da Meranda ta yi a matsayin shugaban, ta dage zaman majalisar tare da da’awar cewa ta zama shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.
Yayin da take bayyana matakinta na yin murabus, Meranda ta ce ta yi hakan ne domin ceto majalisar daga rigingimu da abin kunya da bai kamata ba, tana mai jaddada cewa ta dauki matakin ne don karrama manyan shugabannin siyasa.
Ta yi alkawarin ba za ta rabu da tafarkin mutunci, adalci, rikon amana da hidimar mahaifinta Marigayi Cif Akanni Lawal Taoreed ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki shugaban majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
Babban Kwamishinan Kare Hakkin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya soki hare-haren sama da Amurka ta kai wa jiragen ruwa a yankin Caribbean da Pacific, wanda ya kasance keta dokokin kare hakkin dan adam na duniya.
“An ruwaito cewa an kashe mutane sama da 60 a jerin hare-haren da sojojin Amurka ke kai wa jiragen ruwa a Caribbean da Pacific tun farkon watan Satumba, wadanda ake zargin suna da hannu a safarar miyagun kwayoyi, a cikin wani yanayi da ba su da hujja a karkashin dokokin kasa da kasa,” in ji Volker Turk a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a.
Babban jami’in Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana hare-haren a matsayin “abin da ba za a yarda da shi ba” kuma ya bukaci Washington da ta “kawo karshen irin wadannan hare-hare ta kuma dauki dukkan matakan da suka dace don hana kisan gillar da ake yi wa mutanen da ke cikin wadannan jiragen ruwa ba bisa ka’ida ba, ba tare da la’akari da laifukan da ake zarginsu da aikatawa ba.”
Amurka ta yi ikirarin cewa wadannan ayyuka wani bangare ne na yaki da safarar miyagun kwayoyi da ta’addanci.
Duk da haka, Turk ya nuna cewa yaki da safarar miyagun kwayoyi a kan iyakoki “al’amari ne na tilasta bin doka.”
“Dangane da ƙarancin bayanai da hukumomin Amurka suka bayyana a bainar jama’a, da alama mutanen da ke cikin jiragen ruwan da aka kai hari ba su da wata barazana ga rayukan wasu, kuma ba a yi amfani da karfin soji mai tsanani a kansu ba a karƙashin dokokin kasa da kasa,” in ji shi.
Volker Turk ya yi kira da a “yi bincike mai zaman kansa cikin sauri, kuma ya yi kira ga Amurka da ta yaki fataucin na haramtacciyar hanya ta hanyar kamawa, da gurfanar da wadanda ake tuhuma cikin adalci, da kuma bin ka’ida.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci