Ba ni lokacin cacar baka da El-Rufai —Nuhu Ribadu
Published: 25th, February 2025 GMT
Mashawarcin Shugaban Ƙasa kan Tsaro, Nuhu Ribadu, ya ƙaryata zargin da tsohon abokinsa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi masa na neman takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2031.
A wata hira da aka yi da El-Rufai cikin dare ne tsohon gwamnan Kadunan ya yi zargin cewa Nuhu Ribadu yana da burin tsayawa takarar shugaban ƙasa a babban zaɓe mai zuwa.
A yayin hirar da aka yi da shi a cikin dare a kafar Arise TV ranar Litinin, El-Rufai ya bayyana cewa sun raba jiha da tsohon abokin nasa Nuhu Ribadu da kuma Gwamnan Kaduna mai ci kuma magajinsa, Sanata Uba Sani, yanzu duk ba abokansa ba ne.
Amma martaninsa, a cikin sakon da ya fitar jim kaɗan da ta tsohon gwamnan, Nuhu Ribadu ya ce, ƙarya El-Rufai yake yi cewa ya taɓa yin maganar tsayawarsa takarar 2031 da tsohon gwamnan ko da wani.
NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? Tinubu ne ya sauya ra’ayi kan ba ni muƙamin Minista — El-Rufai“Ba don kada in yi shiru a ɗauka maganar El-Rufai gaskiya ba ce, da na yi watsi da shi. Ni tulin aikin da ke gabana a yanzu ma kaɗai ya ishe ni, balle in tsaya ɓata lokaci ina cacar baka da El-Rufai ko waninsa a kafofin watsa labarai.
Martanin Nuhu Ribadu ga El-Rufai“Duk da cewa ya sha takala ta da caccaka ta, amma saboda mutunta tsohuwar abotarmu, ban taɓa fitowa na aibata shi ba, kun ba zan fara ba.
“Amma ina roƙon jama’a su yi watsi da maganganun da El-Rufai ya yi a kaina.
“Domin kawar da shakku, babu mahalukin da na taɓa magana da shi cewa zan nemi takarar shugaban ƙasa a 2031. Abun da na sa a gaba shi ne ganin Najeriya ta bunƙasa da kuma nasarar Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.
“Saboda haka ina roƙon El-Rufai ya ƙyale Ni in fuskanci aikin yi wa kasa hidima da ke gabana, kamar yadda ni ma ban shiga masa harkokinsa ba.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: takarar shugaban ƙasa zaɓen 2031 El Rufai ya
এছাড়াও পড়ুন:
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Haka kuma, ya zargi Matawalle da karɓar Naira miliyan 300 daga tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari, don a sako ɗaliban, amma ya bai wa ‘yan bindiga miliyan 30 kacal.
APC ta ƙaryata wannan zargi.
Ta kuma bayyana cewa zargin Kaura yana shafar wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar kamar tsohon Gwamna Abdulaziz Yari, wanda yanzu ke wakiltar Zamfara ta Yamma a Majalisar Dattawa.
Jam’iyyar APC ta ƙalubalanci Kaura da ya kawo hujjoji kan wannan zargi da kuma wasu mutane da aka sace a jihar, kamar satar ɗalibai mata 270 daga makarantar Government Girls Secondary School da ke Jangebe a ranar 26 ga watan Fabrairun 2021, da kuma satar ɗaliban Kwalejin Noma da Kiwo da ke Bakura.
APC ta jaddada cewa gwamnatin Matawalle ta yi ƙoƙari wajen yaƙi da ‘yan bindiga da ceto al’ummomi da dama.
Ta bayyana yankuna kamar Gwaram, Kanoma, Kaya, Faru, Janbako, Lilo da Anka, a matsayin wuraren da aka gudanar da ayyukan tsaro da taimako.
Jam’iyyar ta kuma ce tana duba yiwuwar ɗaukar matakin shari’a kan gidan talabijin na Maibiredi TV da ya watsa hirar da ake ganin an shirya don ɓata sunan ministan.
Ta zargi PDP da ƙoƙarin karkatar da hankalin jama’a daga gazawarta ta hanyar yaɗa ƙarya da tayar da fitina don samun moriyar siyasa.
A ƙarshe, APC ta yi kira ga mambobinta da su zauna lafiya da bin doka, inda ta bayar da tabbacin cewa gaskiya za ta fito fili, kuma za a yi adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp