An Bukaci Ma’aikatun Gwamnati Su Rika Yin Kasafin Da Zai Amfani ‘Yan Nijeriya
Published: 28th, January 2025 GMT
Kungiyar masu ruwa da tsakin masana’antu a fannin mai ta Najeriya NEITI da hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, na kokarin kwato kusan dala biliyan shida da kuma wani naira biliyan 66 da gwamnatin tarayya ke bin gwamnatin tarayya bashin.
Sakataren zartarwa na hukumar Mista Orji Ogbonnaya Orji, wanda ya bayyana haka a lokacin kare kasafin kudin 2025 a gaban kwamitin majalisar kan albarkatun man fetur.
Mista Orji Ogbonnaya, ya bayyana cewa tuni hukumar ta gabatar da dukkan rahotannin da ta ke a masana’antar hako mai ga majalisar a wani bangare na matakan tabbatar da samun nasarar kwato kudade daga hukumomin gwamnati.
Ya ce wasu daga cikin abubuwan da hukumar ta sa a gaba a shekarar 2025 sun hada da gudanar da rahoton masana’antu na fannin iskar gas da ma’adinai, da tantance kudaden da doka ta tanada, bincike kan ainihin adadin gidaje mai da ake amfani da su a Najeriya, da kuma aiwatar da binciken ra’ayi jama’a na kasa.
Sakataren zartarwa, ya bayyana cewa NEITI a matsayin hukumar da aka kafa domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkar man fetur da iskar gas a Najeriya ciki har da bangaren ma’adinai, ta sami kasafin kudin shekarar 2025 na Naira biliyan 6.5.
A nasa jawabin shugaban kwamitin kula da albarkatun man fetur na majalisar Alhaji Alhassan Ado Doguwa, ya jaddada muhimmiyar rawar da hukumar ta ke takawa a fannin man fetur, ya kuma ba da tabbacin cewa kwamitin a shirye yake na mara masa baya wajen gudanar da ayyukansa.
Alhaji Alhassan Doguwa, ya shawarci shugabannin hukumar da su ci gaba da sa kaimi ga jin dadin ‘yan Nijeriya a duk lokacin da suke shirya kasafin kudin shekara bisa la’akari da yanayin tattalin arzikin da talakawa ke fuskanta daga sassa daban-daban na kasar nan.
COV: TSIBIRI/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Majalisar Kasa tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Wasu kuma sun jikkata a harin.
Gwamna Sani ya ce kisan rashin imani ne, kuma ya bayyana cewa ya tattauna da Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu don tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.
Ya kai ziyara ga waɗanda suka tsira daga harin a Asibitin Rundunar Sojin Naieriya na 44 da ke Kaduna, sannan ya yaba wa jama’ar Kaduna kan zaman lafiya da kaucewa fitina.
Ya kuma roƙi shugabannin Filato da su hana faruwar irin wannan mummunan lamari.
Gwamnan ya buƙaci hukumomin tsaro da su hanzarta kama masu laifin tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp