Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guteres ya bayyana damuwarsa game da matakin da Shugaba Donald Trump ya dauka na dakatar da taimakon kasashen waje daga Amurka yayin da sabuwar gwamnatin Amurka ke aiwatar da sabbin manufofinta na ketare, kamar yadda mai magana da yawun Guterres ya bayyana.

“Ya yi kira da a yi la’akari da halin da ake ciki don tabbatar da ci gaba da samar da muhimman ayyukan ci gaba da na jin kai ga al’ummomin da ke da rauni a duniya,” in ji Stephane Dujarric ga manema labarai.

” Ya ce akwai al’umomin da suka dogara da wannan tallafin,” inda ya kara da cewa Amurka na “daya daga cikin manyan masu ba da agaji” a duniya.

Kwanaki kadan bayan rantsar da shi, shugaban Amurka Donald Trump ya rattaba hannu kan wata doka, inda ya umurci dukkan hukumomin gwamnatin tarayya da su sanya dokar ta baci na tsawon kwanaki 90 kan taimakon ci gaban kasashen waje da kuma duba shirye-shiryen da ake da su.

“Manufar Amurka ita ce ba za a sake ba da wani taimakon kasashen waje ba ta hanyar da ba ta dace da manufofin ketare na sabon shugaban Amurka ba,”.

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ce an dakatar da duk wani tallafin kudade na shirye-shiryen ba da agajin kasashen waje ban da na manyan kawayenta a Gabas ta Tsakiya, wato Isra’ila da Masar.

Amma umurnin na ranar Juma’a ya kebance tallafin abinci na gaggawa da kuma abubuwan da ke da alaka.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen waje

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta

Kasar Amurka ta sanar da dakatar da bai wa mutanen Nijar bisa ta shiga cikin kasarta har illa masha Allahu.

Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurka ne ya tabbatar da cewa an dakatar da bayar da bisa din ga ‘yan kasar Nijar da suke son shiga cikin kasar, saboda abinda ya kira matsala da ake da ita da gwamnatin Nijar, ba tare da yin Karin bayani ba.

 Sai dai kuma sanarwar ta yi togiya akan jami’an diflomasiyya da sauran jami’an gwamanti,kamar yadda wani sako na diplomasiyya ya nuna a ranar 25 ga watan Yuli.

Wannan matakin na  Amurka ya biyo byan rashin jituwar da ake da shi a tsakanin gwamatin Amurka da gwamnatin Jamhuriyar Nijar. A watan Satumba da ya shude ne dai Amurka ta kammala dauke sojojinta daga kasar Nijar bayan da gwamnatin sojan kasar ta umarce su, su fice daga kasar.

Da akwai sojojin Amurka da sun kai 1000 a cikin jamhuriyar Nijar, da janye su yake a matsayin kwankwasar kan Amurka da rage tasirinta a yammacin Afirka.

Gabanin juyin mulkin da aka yi a kasar dai Amurka tana amfani da wannan cibiyar a abinda take kira fada da ta’addaci a yammacin Afirka. Sai dai kuma hakan bai hana ci gaba da yaduwar ayyukan ta’addanci a cikin kasashen na yammacin Afirka ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  •  Bakai’i: Iran Tana Son Ganin An Yi Taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi
  • Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Kasashen Iran Da Rasha