2025-06-20@16:38:32 GMT
إجمالي نتائج البحث: 1201

«ma ajiyar makamai»:

    Hukumomi na roƙon mazauna yankunan da ambaliya ta shafa da su bi umarnin kwashe jama’a daga yankunan da ke cikin haɗari tare da haɗa kai da jami’an agaji don tabbatar da tsaron lafiyar kowa da kowa. A cikin sanarwar, Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu, tare da jaddada cewa al’ummar...
    Mazauna Babban Birnin Tarayya za su fuskanci katsewar ruwan sha na tsawon makonni biyu, kamar yadda Hukumar Kula da Ruwa ta yankin ta sanar. Rashin ruwan, wanda ya fara ranar Juma’a, 30 ga Mayu, ana sa ran za ta ci gaba har zuwa ranar Juma’a, 13 ga Yuni. Matsalar ta samo asali ne daga ayyukan...
    Dakarun gwagwarmayar kasar Yemen sun bayyana cewa: Za su mayar da jiragen saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila abin ba’a Shugaban majalisar koli ta siyasar kasar Yemen Mahdi al-Mashat, ya tabbatar da cewa: Tsaron sararin samaniyar sojojin kasar Yemen zai iya tunkarar jiragen saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila da suke kai hare-haren wuce gona da iri...
    Maƙabartar Kuka Bulukiya maƙabarta ce mai daɗaɗɗen tarihi a cikin ƙwaryar birnin Kano, wadda bayanai suka nuna an shafe sama da shekara 500 ana binne mamata a cikinta. Wannan daɗaɗɗiyar maƙabarta tana da matuƙar muhimmanci musamman la’akari da yawan unguwannin da suka kewaye ta da yawan mutanen da aka binne a cikinta da kuma fitattun...
    Sojoji sun yi nasarar cafke wani mutum da ake zargi dan ta’adda ne tare da gano ma’adanar makamai a yayin wani samame da suka yi a Ƙaramar Hukumar Bassa ta Jihar Filato. Binciken farko ya nuna cewa wanda aka kama ɗin yana da alaƙa da wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ke da alhakin kisan...
    Kungiyar ‘yan ta’adda ta Daesh ta dauki alhakin kai hari kan dakarun gwamnatin Hayat Tahrir al-Sham (HTC) na kasar Siriya, wanda shi ne irinsa na farko a kan tsoffin kawayenta tun bayan hambarar da gwamnatin Bashar al-Assad na Siriya. A wata sanarwa da ta fitar kungiyar ta ce ta sanya “bama-bamai” kan motar dakarun da...
    Babbar jami’a a hukumar kiwon lafiya ta kasar Sin Shen Haiping, ta ce a shekarun baya bayan nan koshin lafiyar yaran kasar Sin na kara inganta. Jami’ar wadda ta bayyana hakan ga wani taron manema labarai a yau, ta ce a shekarar 2024, alkaluman mace-macen jarirai a kasar ya ragu zuwa jariri hudu cikin duk...
    Rahotanni daga kasar ta DRC sun ambaci cewa an ga tsohon shugaban kasar Joseph Kabila a jiya Alhamis a garin Goma wanda yake a karkashin ikon ‘yan tawayen kungiyar M23. Majiyar malaman addinin kirista a yankin ce ta sanar da cewa, ta gayyace shi ne domin ya shiga Tsakani a kawo karshen yakin da ake...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Yawan mutanen da suka rasu a sakamakon mummunar ambaliyar ruwan sama a yankin Ƙaramar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja ya ƙaru zuwa 88. Shugaban Sashen Ayyuka na Hukumar ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Husseini Isah, ne ya sanar da haka a ranar Juma’a. Ya ce, “adadin mamatan na ci gaba da ƙaruwa,...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran yayi tsokaci kan hasashe game da kusancin cimma yarjejeniyar nukiliyar da ke gudanarwa tsakanin Amurka da Iran Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Hanyar diflomasiyya tana bukatar a dage dukkan takunkumai da aka kakabawa Iran da kuma mutunta hakkin mallakar makamashin nukiliyar Iran, yana mai cewa:...
    Mai ba da shawara ga jagoran juyin juya halin Musulunci ya mayar da martani ga barazanar shugaban kasar Amurka kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran Ali Shamkhani mashawarcin Jagoran juyin juya halin Musulunci a fagen siyasa ya jaddada cewa: Iran kasa ce mai cin gashin kanta mai tsayayyen tsarin tsaro, al’umma masu tsayin daka, da jajayen...
    A wannan zango na shekaru biyun Tinubu, ma’aikatar yada labarai ta kasa; ita ce ginshikin aiwatar da wadannan dabaru da tsare-tsare, musamman ta fuskar sake fasalin hukumomi, aikewa da sakwannin jan kunne da ladabtarwa da kuma jin ra’ayoyin daidaikun mutane, wanda hakan ya bai wa gwamnatin damar sanin matsalolin ‘yan kasa da kuma hanyoyin da...
    Wasu mutum 12 ’yan gida daya da almajirai sama da 50 na cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwan da ta afka wa yankin Tiffin Maza da Anguwan Hausawa na karamar hukumar Mokwa a jihar Neja a ranar Laraba. Ambaliyar, wacce ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka a daren na...
    Ambaliyar dai, ta afku ne sakamakon mamakon ruwan sama da aka shafe sa’o’i da dama yana sauka a daren Laraba.   Wani mazaunin garin, Mohammed Usman ya ce tuni aka fara tsamo gawarwaki da dama a cikin ruwan, amma wasu da dama ba a iya ganin su ba musamman a wuraren da gidaje suka nutse....
    Shugaban kwamitin kungiyar Tarayyar Afrika (AU) Mahmoud Ali Youssouf, ya nanata godiyar kungiyar bisa irin goyon bayan da kasar Sin ke ba ta da ma kasashen Afrika a muhimman bangarori kamar na cinikayya da raya ababen more rayuwa da aikin gona da kiwon lafiya da bunkasa kwarewar jami’ai. Wata sanarwa da aka fitar jiya Laraba,...
    Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake dasuwa a cikin shirimmu na duniyarmu a yau shiri wanda yake kawo maku labarai masu muhimmaci a makon da ya gabata, wanda suka shafi siyasa tattalin arziki zamnatakewa tsaro da sauransu. Inda muka yi masu karin bayani sannan mu ji ra’ayin masana dangane da su...
    Mutanen da ya zuwa yanzu ba a kai ga tantance adadinsu ba sun rasa rayukansu sakamakon wata ambaliyar ruwa da ta afka wa garin Mokwa na jihar Neja. Mazauna yankin sun kuma ce babbar hanyar da ta hada arewaci da kudancin Najeriya da ta bi ta yankin ita ma ambaliyar ta yanke ta. Kodayake dai...
    An ngudanar da taron harkokin tsaro na kungiyar BRICS karo na 13TH inda wakilai da kasashen Iran da sauran kasashen kungiyar a birnin Mosco a ranar Laraba 28 ga watan Mayun da muke ciki. Shafin yanar gizo na labarai AfricaNews ya bayyana cewa babbakan sakataren majalisar tsaro na kasar Iran Ali Akbar Ahmadian da Shugaban...
    Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kuma kawayenta a wajen kungiyar sun gudanar da taro a birnin Riyad na kasar Saudia inda suka tattauna kan yawan man fetur da zasu haka daga shekara da ta 2027. Shafin yada labarai na tanar gizo na kasar Saudia Arab News ya bayyana cewa wannan yana daga cikin...
    Kasashen kungiyar ‘ the Association of Southeast Asian Nations’ ko ASEAN ta yi allawadai da kisan kiyashiun da ke faruwa a zirin gaza, sannan ta bukaci kasashen duniya su dauki matakan da suka dace don dawo da doka da oda na kasar Falasdinu da aka mamaye, a kuma kawo karshen kisan kiyashin da ke faruwa...
    A wani babban ci gaba na kawo sauyi a tsarin kiwon lafiyar Najeriya, gwamnatin tarayya ta yi  ta kaddamar da ayyuka 16 a asibitin masu tabin hankali na gwamnatin tarayya dake Kware a jihar Sokoto.   Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar, Ministan Kasa a ma’aikatar Lafiya da walwalar jama’a, Dokta Iziak Salako, ya...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A yau shekara biyu ke nan cif  tun bayan da  shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi mulkin Najeriya a matsayin shugaban ƙasa na 16 tun bayan samun ‘yancin kai.   Daya daga cikin abubuwan da shugaban kasar ya fara yi yayin jawabin karbar mulkin shi ne sanar da...
    Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; Harin da “Isra’ila” ta kai wa filin saukar jiragen saman Sanaa, manufarsa  ita ce yin matsin lamba akan matsayarmu ta taimakawa al’ummar Falasdinu da ake zalunta.” Sayyid Abdulmalik al-Husi ya kara da cewa;  Komai girman hare-haren da Isra’ilan za ta kai ba zai...
    Shugaban rundunar mayakan sama ta kasa,Air Marshal, Hassan Abubakar, ya bukaci tsoffin daliban makarantar ‘ya’yan sojoji dake Zaria watau NMS da su kasance masu kwazo da da’a a duk inda suke kamar yadda suka koya a makarantar. Ya bayyana haka ne lokacin da ya ke jawabi a matsayin Babban bako na musamman a wurin bukin...
    Babbbar Kotun Tarayya da ke Kano ta yanke wa fitacciyar ’yar Tiktok, Murja Ibrahim wacce aka fi sani da Murja Kunya hukunicn daurin watanni shida a kurkuku. Alƙalin kotun Mai Shari’a Simon Amobida ya kuma ba wa Murja zabin biyan tarar Naira dubu 50. Ya ce saboda yawan mabiyanta a shafinta na Tiktok, an nada...
    A cikin wani mataki na ci gaba da sauya fasalin bangarorin noma da kiwo, Gwamnatin Jihar Jigawa na shirin kulla yarjejeniyar hadin gwiwa da daya daga cikin manyan kamfanonin kiwon kaji na kasar Indiya, wato Srinivasa Farms. Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Jigawa, Hamisu Mohammed...
    Kungiyar agaji ta red crescent ta iran da kuma kungiyar red cross ta kasar Saliyo sun cimma yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu. An cimma wannan ne a yayin ziyarar da babban daraktan kula da lafiya na kungiyar agaji ta Red Crescent na Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya kai Saliyo tare da gudanar da tarurruka da...
    Ya ce, ana gudanar da aikin binciken ne a fadin jihohi 11 inda aka kama wadanda ake zargin a Bauchi, Benuwe, Borno, Ebonyi, Enugu, Lagas, Filato, Kaduna, Ribas, Taraba da kuma babban birnin tarayya, Abuja. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura...
    Ya ce jami’an FEMD, FRSC da ‘yansanda sun gaggauta zuwa wurin domin gudanar da aikin ceto. Mohammed ya ja kunnen direbobi da su tabbatar motocinsu na cikin ƙoshin lafiya kafin su hau hanya. Ya kuma shawarci jama’a da su rika kiran lambar gaggawa 112 idan wani lamari ya faru. Wannan hatsari ya ƙara tayar da...
    Dakarun sojojin Najeriya sun dakile wani harin hadin gwiwa da ‘yan ta’addar Boko Haram da ISWAP suka kai a yankin Marte da ke jihar Borno, inda suka kashe wasu da dama daga cikin maharan. Majiyar leken asirin hedikwatar sojan Najeriya ta tabbatar  da cewa harin ya faru ne da misalin karfe 1:35 na wayewar safiyar...
    Falasdinawa da dama ne suka ji rauni a jiya Talata a lokacinda yahudawan Sahyoniyya suka bude rumbunajiyar kayakin abinda ga Falasdinawa a garin Rafah na kudancin gaza. Shafin yanar gizo na Afirka News ya bayyana cewa dubban Falasdinawa wadanda suka yi kwanaki 90 basu sami abinci ba saboda rufe kofar shiar da abinci zuwa gaza....
    Kungiyar kare hakkin bil’aama ta “Amnesty International” ta bayyana cewa; mai yiyuwa ne kungiyar ‘yan tawaye ta m23 da kuma sojojin gwamnatin DRC sun aikata laifukan yaki. A wani rahoto da aka buga a jiya Talata, kungiyar kare hakkin bil’adam ta ce; Kungiyar M23 wacce take samun goyon bayan kasar Rwanda ta kashe mutane da...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Iran ba za ta daina sarrafa sinadarin Uranium a kowane hali ba Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya tabbatar a wata hira da tashar CNN ta Amurka cewa: Iran ba za ta taba yin watsi da hakkinta na tace sinadarin Uranium a kowane hali ba....
    Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da wasikar taya murna ga taron kasa karo na tara na kungiyar yara jagorori na kasar Sin (CYP), wanda aka bude a yau Talata a birnin Beijing. Xi ya jaddada muhimmancin ganin kungiyar ta bi sawun jam’iyyr kwaminis ta kasar Sin a da kuma yaye hazikai masu gina...
    Duk tare da yakin da suke fafatawa a Gaza, dimbin yahudawan sahyoniyya  masu bauta sun kutsa cikin masallacin Al-aksa da ke birnin Qudus inda suka gudanar da bukukuwan addinu a jiya Litinin. Shafin yanar Gizo na labarai ‘Arab News’ ya bayyana cewa, bakin na addini, farin ciki ne da kwace gabacin birnin Qudus daga hannun...
    Sojojin kasar Yemen sun sake kai wani hari da makali mai linzami da safiyar yau Talata wanda ya sa jiniyar gargadi ta kada a cikin yankuna da dama na HKI. Wannan dai shi ne karo na 3 a cikin sa’o’i 24 da kungiyar Ansarullah ta Yemen ya harba wa HKI makamai masu linzami. Sojojin HKI...
    Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayya ta buƙaci al’ummar da ke kewayen hanyar Mararaba zuwa Nyanya su kwantar da hankalinsu bayan jin ƙarar wani abu da ya fashe a yammacin ranar Litinin. Lamarin ya faru ne a wata tashar bas da ke kusa da barikin sojoji na Mogadishu a kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya. A wata...
    Iran ta yi kira da a karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka bisa tsarin yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar A yayin bikin karo na 62 na kafuwar kungiyar Tarayyar Afirka da aka gudanar a birnin Tehran, ministan harkokin wajen kasar Iran Seyyed Abbas Araghchi ya jaddada aniyar kasar Iran na karfafa hadin...
    Kasar Spain ta bukaci kasashen duniya dasu kakabawa Isra’ila taklunkumi saboda ci gaba da yin fatali da kiraye-kirayen da ake matana tadakatar da yakin da take a Gaza. Ministan harkokin wajen Spain José Manuel Albares ya ce kamata ya yi kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi domin kawo karshen munanan hare-haren soji a zirin Gaza...
    Shugaban kasar Kenya William Samoei Ruto ya ziyarci kasar Sin daga ran 22 zuwa 26 ga watan Afrilun da ya gabata, bisa gayyatar da takwaransa na Sin Xi Jinping ya yi masa. Yayin ziyararsa, shugabannin biyu sun kai ga matsaya daya kan daga matsayin dangantakar kasashen biyu zuwa hulda mai makoma ta bai daya a...
    Ya ce: “Ya kamata ku nazarci Shugaban Ƙasa sosai. Za ku iya faɗin ra’ayoyin ku; zai saurare ku, amma a ƙarshe shawarar da zai yanke tasa ce. Ina ganin ya dace mu gane hakan.”   Yayin da yake bayani kan taken taron, ministan ya ce Shugaba Tinubu na da cikakkiyar niyya wajen aiwatar da Shirin...
    Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikn Na’im Kassim ya bayyana cewa; Idan har gwamnatin kasar ta gajiya wajen yin abinda ya rataya a wuyanta na aiki da tsagaita wutar yaki, to gwgawarmaya tana da wata hanyar da za ta yi aiki da ita akan ‘yan mamaya. Sheikh Na’im Kassim wanda ya gabatar da...
    Jaridar ” Up Isra’el” ta buga labarin cewa; shugaban cibiyar Ayyukan Agaji A Gaza” wacce ke karkashin Amurka da Isra’ila”  ya yi murabus saboda abinda ya kira rashin gaskiya da ‘yanci a cikin Shirin. Jaridar ta ambato  Jake Wood yana cewa; Ba abu ne mai yiyuwa ba a aiwatar da Shirin agaji a Gaza, sannan...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Baki a Nijeriya da abokansu Sinawa sun nishadantu yayin da suka halarci taron gabatar da fasahar hada shayi ta 2025 da al’adun Yaji, wanda aka yi jiya Asabar a Abuja babban birnin kasar. An gudanar da taron ne a cibiyar raya al’adu ta kasar Sin da hadin gwiwar cibiyar raya al’adu ta lardin Zhejiang, wadda...
    Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran ya bayyana cewa: Suna yin aiki ne bisa maslahar kasa, kuma ba su yarda da karbar umarni daga waje ba Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran, Mohammad Islami, ya ce Iran tana dogara ne kan manufofinta na kasa da kuma manufofinta na koli, kuma ba zata yarda wasu kasashen...
    Gwamnatin Sudan ta bayyana cewa: Sabbin takunkuman da Amurka ta kakaba mata, bakar siyasa ce ta nemen bata mata suna A cikin wata sanarwa da gwamnatin Sudan ta fitar, ta yi Allah-wadai da matakin da gwamnatin Amurka ta dauka na kakaba mata sabbin takunkumai, tana mai bayyana hakan a matsayin maimaita kura-kurai irin na baya...
    A halin yanzu, a gonaki masu samar da shinkafar da aka tagwaita a Madagascar, ana farin cikin girbar shinkafa mai armashi. Masanan aikin gona na kasar Sin sun bi sahun Yuan Longping don tabbatar da burinsa na hadin gwiwa da manoman kasar wajen samar da isashen hatsi. (Mai zane da rubutu: MINA)   Daga...
    Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin taimaka wa wata yarinya ’yar shekara 14 da aka tilasta yi mata auren dole a Jihar Taraba. Kwamishinar Ma’aikatar Mata da Walwala, Asma’u Iganus, ta ce yarinyar ta nemi taimako bayan da kakanta ya ɗaura mata aure da wani mutum a matsayin mata ta huɗu. An kama Hakimi kan zargin...