Sin Da Vietnam Na Fitar Da Sabuwar Taswirar Zamanintar Da Al’Ummunsu Cikin Hadin Gwiwa
Published: 16th, April 2025 GMT
Wadannan shawarwari guda 6 sun samar da makoma mai haske ga zamamintar da al’ummun kasashen biyu da yawansu ya wuce biliyan 1.5, da ma kafa kyakkyawar makomarsu ta bai daya.
Hadin gwiwar kasashen biyu a bangaren ciniki ingantaccen karfi ne na ingiza huldarsu. A cikin shekaru 20 a jere da suka gabata, Sin ta kai matsayin abokiyar ciniki mafi girma ga Vietnam, kuma Vietnam ta zama abokiyar ciniki mafiya girma ga kasar Sin a mambobin kungiyar ASEAN.
Yayin ziyarar aikinsa a wannan karo, Xi Jinping da Tô Lâm sun halarci bikin kaddamar da tsarin hadin gwiwar kasashen biyu wajen kafa layin dogo tsakaninsu. Ban da wannan kuma, bangarorin biyu sun kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa har 45 tsakaninsu, ciki har da na kara tuntuba, da mu’ammala tsakaninsu, da fasahar AI, da aikin binciken kwastam, da cinikin kayayyakin aikin gona, da zaman rayuwar jama’a da sauransu.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da labarin cewa, ziyarar Xi a Vietnam a wannan karo, za ta gaggauta hadin gwiwar kasashen biyu a bangaren ciniki da tsarin samar da kayayyaki.
Idan mun yi hangen nesa a tarihi, ingantacciyar kyakkyawar makomar al’ummun biyu ta bai daya ta amfani al’ummun kasashen biyu da yawansu ya zarce biliyan 1.5, kuma tana kawowa duniya tabbaci, da dorewa da ake matukar bukata a halin yanzu duba da sauye-sauyen da ake fuskanta. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Haramta Sabuwar Hisbah Da Ganduje Ke Shirin Ƙirƙirowa
Gwamnatin Jihar Kano ta fitar sanarwar umarnin haramta kafa wa, da ɗaukar aiki da gudanar da duk wata ƙungiyar Hisbah mai zaman kanta a jihar, inda ta dakatar da ƙungiyar Independent Hisbah Fisabilillahi da tsohon gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ke shirin Ƙirƙirowa.
Kwamishinan yaɗa labarai ne ya sanar da hakan a taron manema labarai a Kano, yana mai cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu kan umarnin ne domin kare zaman lafiya da kuma kare sahihancin Hukumar Hisbah ta Jihar Kano da doka ta kafa.
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano Ƙirƙirar Hisbah Mai Zaman Kanta: Kungiyar Lauyoyi ‘Yan Kano Ta Shigar Da Tinubu ƘaraUmarnin ya bayyana cewa duk wani yunƙuri na ɗaukar aiki, da horarwa ko tura mutane don kafa wata Hisbah ta daban haramun ne, kuma ba shi da inganci a doka. Gwamnati ta umurci jami’an tsaro su dakatar da duk wani motsi da kuma bincikar masu ɗaukar nauyin ƙungiyar.
ADVERTISEMENTGwamnatin ta kuma gargadi jama’a da su guji shiga ko tallafa wa ƙungiyar da aka haramta, tana mai cewa duk wanda ya bin umarnin zai fuskanci hukunci bisa dokokin jihar kuma umarnin ya fara aiki nan take.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA