Sin Da Vietnam Na Fitar Da Sabuwar Taswirar Zamanintar Da Al’Ummunsu Cikin Hadin Gwiwa
Published: 16th, April 2025 GMT
Wadannan shawarwari guda 6 sun samar da makoma mai haske ga zamamintar da al’ummun kasashen biyu da yawansu ya wuce biliyan 1.5, da ma kafa kyakkyawar makomarsu ta bai daya.
Hadin gwiwar kasashen biyu a bangaren ciniki ingantaccen karfi ne na ingiza huldarsu. A cikin shekaru 20 a jere da suka gabata, Sin ta kai matsayin abokiyar ciniki mafi girma ga Vietnam, kuma Vietnam ta zama abokiyar ciniki mafiya girma ga kasar Sin a mambobin kungiyar ASEAN.
Yayin ziyarar aikinsa a wannan karo, Xi Jinping da Tô Lâm sun halarci bikin kaddamar da tsarin hadin gwiwar kasashen biyu wajen kafa layin dogo tsakaninsu. Ban da wannan kuma, bangarorin biyu sun kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa har 45 tsakaninsu, ciki har da na kara tuntuba, da mu’ammala tsakaninsu, da fasahar AI, da aikin binciken kwastam, da cinikin kayayyakin aikin gona, da zaman rayuwar jama’a da sauransu.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da labarin cewa, ziyarar Xi a Vietnam a wannan karo, za ta gaggauta hadin gwiwar kasashen biyu a bangaren ciniki da tsarin samar da kayayyaki.
Idan mun yi hangen nesa a tarihi, ingantacciyar kyakkyawar makomar al’ummun biyu ta bai daya ta amfani al’ummun kasashen biyu da yawansu ya zarce biliyan 1.5, kuma tana kawowa duniya tabbaci, da dorewa da ake matukar bukata a halin yanzu duba da sauye-sauyen da ake fuskanta. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ministan tsaron Iran na Ziyara a UAE don karfafa dangantakar tsaro tsakanin kasashen yankin
Ministan tsaron Iran Birgediya Janar Aziz Nasirzadeh ya kai ziyarar aiki a Hadaddiyar Daular Larabawa don inganta dangantakar soja da kuma huldar tsaro a yankin.
Nasirzadeh ya jagoranci wata babbar tawaga, wadda ta isa Dubai a ranar Litinin bisa gayyatar takwaransa na Hadaddiyar Daular Larabawa.
Ministan tsaron Iran yana shirin yin tattaunawa da jami’an Hadaddiyar Daular Larabawa da kuma halartar taron Dubai Airshow na 2025, wanda aka shirya gudanarwa a tsakanin 17-21 ga Nuwamba.
Ziyarar ta zo ne a karkashin tsarin diflomasiyyar tsaron Iran kuma tana da nufin inganta huldar yanki da kuma gano damar yin hadin gwiwa a fannoni daban-daban.
A lokacin rangadin baje kolin, an shirya cewa ministan tsaron na Iran zai yi tarurruka da jami’an tsaro daga kasashe da dama.
Bikin Dubai Airshow na 2025 zai karbi bakuncin masu baje kolin sama da 1,500, wadanda suka hada da sabbin masu baje kolin sama 440, masu Ziyara da ‘yan kasuwa 148,000, da kuma wakilai 490 na sojoji da fararen hula daga kasashe 115.
Za a nuna sama da jiragen sama 200, ciki har da jiragen sama na kasuwanci, na soja, na liken asirri, jiragen sama marasa matuki, da kuma fasahar zamani, wanda shi ne baje koli irinsa mafi girma a tarihi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Masu shigar da kara na ICC sun bukaci hukuncin daurin rai da rai a kan kwamandan RSF November 18, 2025 MDD ta amince da kudurin tura dakarun kasa da kasa zuwa Gaza November 18, 2025 Congo ta tsawaita haramcin fataucin ma’adinai a gabashin kasar November 18, 2025 Rasha: An dakile wani yunkurin kisan gilla kan Sakataren Majalisar Tsaron kasa November 18, 2025 Aref: Iran Tana Da Kyakkyawar Alaka Da Mambobin Kungiyar Hadin Gwiwa Ta Shanghai {SCO} November 17, 2025 Na’ini: Jagora Ne Da Kansa Ya Jagoranci Lamurra A Lokacin Yakin Kwanaki 12 Da Aka Kaddamar Kan Iran November 17, 2025 Mahukuntan Gaza Sun Yi Gargadin Bullar Bala’in Jin Kai A Yankin Da Ba A Taba Ganin Irinsa Ba November 17, 2025 Sheikh Na’im: Gwamnatin Lebanon Zata Yi Babban Kuskure Matukar Tabi Hanyar Sassauci November 17, 2025 Rushewar Ramukan Hako Ma’adinai Ta Kashe Mutane 32 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango November 17, 2025 Alummar Kasar Ecodo Sun yi Watsi Da Batun Sake Dawo Da Sansanin Sojin Amurka A Kasar November 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci