Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna
Published: 14th, April 2025 GMT
Da yake jawabi a madadin shugaban kasa, Gwamna Uba Sani ya bayyana mahimmancin hanyar wadda ta hada babban birnin tarayya da jihohi sama da 12 dake fadin shiyyar Arewa ta tsakiya, Arewa maso Yamma, da Arewa maso Gabas.
A yayin taron da aka yi a Jere a karamar hukumar Kagarko a ranar Lahadin da ta gabata, Gwamna Sani ya bayyana cewa, an yi biris da aikin hanyar na tsawon shekaru da dama, wanda ya janyo asarar rayuka da kuma illa ga ci gaban tattalin arzikin yankin.
Sai dai Gwamnan ya kafa uzurin cewa, baya ga kudade, rashin tsaro da ake fama da shi a hanyar Kaduna zuwa Abuja a lokacin ne kamfanin Berger ya ki zuwa wurin domin ci gaba da aiki.
Amma a yanzu, hanyoyin da aka bi na magance matsalar tsaro yana haifar da sakamako mai kyau, domin masu ababen hawa na iya bin hanyar ba tare da fargabar an kai musu hari ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi
Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani, ya amince da aiwatar da ƙarin kashi 70 a albashin ma’aikatan dukkanin makarantun gaba da sakandare na gwamnati da ke jihar.
Sabon tsarin albashin na CONPCASS/CONTEDISS 2024 wanda zai fara aiki daga Oktoban 2025, na daga cikin kokarin gwamnatinsa na inganta walwalar ma’aikata da farfaɗo da harkar ilimi a jihar.
Fashewar tankar mai ta yi ajalin mutum 30 a Neja Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsaAmincewar na zuwa ne bayan wani muhimmin zama da aka gudanar tsakanin gwamnan da shugabannin ƙungiyoyin ma’aikatan manyan makarantu (JUTIKS), wanda hakan ya kai ga janye yajin aikin da aka shafe wata guda ana yi.
Taron wanda Ƙungiyar Ƙwadago ta NLC ta shirya kuma aka gudanar a fadar gwamnatin Kaduna, ya samu halartar shugabannin ƙungiyoyi daga Nuhu Bamalli Polytechnic da ke Zariya, da Kwalejin Ilimi ta Gidan Waya, da kuma Kwalejin Nazarin Jinya da Ungozoma ta Kaduna.
Ana iya tuna cewa, tun a ranar 30 ga watan Satumban da ya gabata ne ma’aikatan manyan makarantun suka tsunduma yajin aikin neman a aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS/CONTEDISS na 2009, da kuma inganta fansho da walwalar ma’aikata gaba ɗaya.
A wani taron manema labarai da shugabannin ƙungiyoyin suka gudanar, sun yaba da jajircewar gwamna Uba Sani wajen kare haƙƙin ma’aikata da bai wa ilimi fifiko.
Haka kuma, sun jinjina wa gwamnatin bisa rage kuɗin makaranta da kashi 50% a dukkanin manyan makarantu, da kuma gyare-gyaren gine-gine da kayan aiki da ake ci gaba da yi.