Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-04@00:51:10 GMT

NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna

Published: 13th, April 2025 GMT

NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna

 

Kungiyar Kwararrun Masu Fasahar Injiniya ta Ƙasa (NATE) ta rantsar da sabbin shugabannin reshen Jihar Kaduna da za su jagoranci harkokin kungiyar a jihar.

 

Mataimakin Shugaban Yankin Arewa maso Yamma na NATE, Injiniya Bala Muhammad, yayin bikin rantsarwa da aka gudanar a Kaduna, ya bukaci sabbin shugabannin da su fifita haɗin kai da ci gaban ƙungiyar.

 

Sabbin shugabannin da aka rantsar sun hada da: Injiniya Audu John a matsayin Shugaba, AbdulKadir Julde a matsayin Mataimakin Shugaba, sannan Williams Okonkwu a matsayin Sakataren reshen.

 

Sauran su ne Sim Marca Maikege a matsayin Ma’ajin Kuɗi, AbdulGaniu Isah a matsayin Sakataren Kuɗi, da Racheal Ovbiagele a matsayin Sakataren Fasaha.

 

Haka kuma, Engr. Ishaya Buba daga Radio Nigeria Kaduna ya zama Jami’in Hulɗa da Jama’a, Khadijah Abdullahi a matsayin Ko’odinetan Mata, sannan Aliyu Ibrahim Usman a matsayin Sakataren Membobinsu.

 

Matsayin Mai Bincike (Auditor) da Mataimakin Sakatari suna nan a buɗe, ba a cike su ba tukuna.

 

A jawabinsa na kama aiki, sabon Shugaban, Injiniya Audu John, ya jaddada muhimmancin jajircewar mambobi, musamman ta fuskar biyan kuɗin zama dan kungiya da kuma kuden cigaba da zama dan kungiya wato (check-off dues).

Ya ce babu wata ƙungiya da za ta samu ci gaba idan ba tare da sadaukarwar mambobinta ba, kuma za su baiwa wannan bangare muhimmanci sosai.

 

Injiniya Audu John ya kuma bayyana shirin hadin gwiwa da manyan abokan hulɗa, musamman a sashen masana’antu, gwamnati da masu zaman kansu, domin tabbatar da cewa mambobin kungiyar sun samu wakilci da tallafi yadda ya kamata.

 

A cewarsa, shugabannin da suka gabata sun fara irin wannan aiki ta hanyar kai ziyarar girmamawa zuwa kamfanonin Nocaco Nigeria Limited da Hukumar Albarkatun Ruwa domin tantance mambobi da kuma farfado da hulɗar hadin gwiwa.

 

Shugaba Audu ya yaba wa Kwamitin Zaɓe karkashin jagorancin Engr. Silas Oluyori bisa gudanar da zaɓe mai tsafta, adalci da gaskiya duk da kalubalen da suka fuskanta.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Yanki Arewa maso Yamma, Injiniya Bala Muhammad, wanda Jami’in ƙasa na NATE, Injiniya Lukman Sani ya wakilta, ya bayyana cewa reshen Kaduna ne tushen dukkanin rassan NATE a yankin Arewa maso Yamma, amma har yanzu yana fama da kalubale.

 

Ya bukaci sabbin shugabannin su yi aiki tare da juna don dawo da karfin da kuzarin reshen Kaduna kamar yadda aka san shi a da.

 

Ya taya kwamitin zaɓe murna bisa gudanar da zaɓen cikin nasara, tare da tabbatar da ci gaba da tallafa musu don cigaban reshen jihar.

 

Tun da farko a jawabin sa, Shugaban Kwamitin Zaɓe, Engr. Silas Oluyori, ya gode wa duk masu ruwa da tsaki a kungiyar bisa goyon bayan da suka bayar, wanda ya taimaka sosai wajen shawo kan matsalolin da suka fuskanta a lokacin shirya zaɓen.

 

A zantawa da manema labarai, sabon Jami’in Hulɗa da Jama’a, Engr. Ishaya Buba, na gidan Radio Nigeria Kaduna ya bayyana cewa sabbin shugabannin za su kawo sauyi mai amfani wanda zai ɗaga darajar ƙungiyar zuwa mataki mafi girma.

Ya ce, cancanta da jajircewar sabbin shugabannin na nuna alamar cewa za su taka rawa ta kwarai wajen jagoranci da kawo ci gaba mai ma’ana ga reshen Kaduna.

 

REL: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnati Kaduna Jihar Rantsarda

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

’Yan bindiga kimanin guda huɗu dauke da makamai sun kai hari a garin Eruku da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, inda suka sace wani manomi mai suna Mista Aasaru.

Rediyon Najeriya ya ruwaito  cewa wannan hari shi ne na biyu da aka kai wa garin Eruku cikin wata guda, kuma ya faru ne kwanaki kaɗan bayan gwamnatin tarayya ta samu ’yantar da mambobin Cocin Christ Apostolic Church (CAC) 38 da aka yi garkuwa da su a yankin.

Majiyar da ta yi magana da Rediyon Najeriya ta ce ’yan bindigar sun farmaki Aasaru ne a wani daji da ke kan hanyar Koro.

Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sandan jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewarta, jami’an ’yan sanda daga sashin Eruku sun karɓi korafi a ranar Lahadi cewa wasu mutane huɗu dauke da makamai sun kutsa wata gona a kan hanyar Koro, Eruku, inda suka sace wani Mista Aasanru mai shekaru 40.

Ejire-Adeyemi ta ce ana cigaba da ƙokari wajen ganin an kubutar da manomin da aka sace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro
  • Tinubu ya naɗa Janar CG Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma