Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@03:02:56 GMT

NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna

Published: 13th, April 2025 GMT

NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna

 

Kungiyar Kwararrun Masu Fasahar Injiniya ta Ƙasa (NATE) ta rantsar da sabbin shugabannin reshen Jihar Kaduna da za su jagoranci harkokin kungiyar a jihar.

 

Mataimakin Shugaban Yankin Arewa maso Yamma na NATE, Injiniya Bala Muhammad, yayin bikin rantsarwa da aka gudanar a Kaduna, ya bukaci sabbin shugabannin da su fifita haɗin kai da ci gaban ƙungiyar.

 

Sabbin shugabannin da aka rantsar sun hada da: Injiniya Audu John a matsayin Shugaba, AbdulKadir Julde a matsayin Mataimakin Shugaba, sannan Williams Okonkwu a matsayin Sakataren reshen.

 

Sauran su ne Sim Marca Maikege a matsayin Ma’ajin Kuɗi, AbdulGaniu Isah a matsayin Sakataren Kuɗi, da Racheal Ovbiagele a matsayin Sakataren Fasaha.

 

Haka kuma, Engr. Ishaya Buba daga Radio Nigeria Kaduna ya zama Jami’in Hulɗa da Jama’a, Khadijah Abdullahi a matsayin Ko’odinetan Mata, sannan Aliyu Ibrahim Usman a matsayin Sakataren Membobinsu.

 

Matsayin Mai Bincike (Auditor) da Mataimakin Sakatari suna nan a buɗe, ba a cike su ba tukuna.

 

A jawabinsa na kama aiki, sabon Shugaban, Injiniya Audu John, ya jaddada muhimmancin jajircewar mambobi, musamman ta fuskar biyan kuɗin zama dan kungiya da kuma kuden cigaba da zama dan kungiya wato (check-off dues).

Ya ce babu wata ƙungiya da za ta samu ci gaba idan ba tare da sadaukarwar mambobinta ba, kuma za su baiwa wannan bangare muhimmanci sosai.

 

Injiniya Audu John ya kuma bayyana shirin hadin gwiwa da manyan abokan hulɗa, musamman a sashen masana’antu, gwamnati da masu zaman kansu, domin tabbatar da cewa mambobin kungiyar sun samu wakilci da tallafi yadda ya kamata.

 

A cewarsa, shugabannin da suka gabata sun fara irin wannan aiki ta hanyar kai ziyarar girmamawa zuwa kamfanonin Nocaco Nigeria Limited da Hukumar Albarkatun Ruwa domin tantance mambobi da kuma farfado da hulɗar hadin gwiwa.

 

Shugaba Audu ya yaba wa Kwamitin Zaɓe karkashin jagorancin Engr. Silas Oluyori bisa gudanar da zaɓe mai tsafta, adalci da gaskiya duk da kalubalen da suka fuskanta.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Yanki Arewa maso Yamma, Injiniya Bala Muhammad, wanda Jami’in ƙasa na NATE, Injiniya Lukman Sani ya wakilta, ya bayyana cewa reshen Kaduna ne tushen dukkanin rassan NATE a yankin Arewa maso Yamma, amma har yanzu yana fama da kalubale.

 

Ya bukaci sabbin shugabannin su yi aiki tare da juna don dawo da karfin da kuzarin reshen Kaduna kamar yadda aka san shi a da.

 

Ya taya kwamitin zaɓe murna bisa gudanar da zaɓen cikin nasara, tare da tabbatar da ci gaba da tallafa musu don cigaban reshen jihar.

 

Tun da farko a jawabin sa, Shugaban Kwamitin Zaɓe, Engr. Silas Oluyori, ya gode wa duk masu ruwa da tsaki a kungiyar bisa goyon bayan da suka bayar, wanda ya taimaka sosai wajen shawo kan matsalolin da suka fuskanta a lokacin shirya zaɓen.

 

A zantawa da manema labarai, sabon Jami’in Hulɗa da Jama’a, Engr. Ishaya Buba, na gidan Radio Nigeria Kaduna ya bayyana cewa sabbin shugabannin za su kawo sauyi mai amfani wanda zai ɗaga darajar ƙungiyar zuwa mataki mafi girma.

Ya ce, cancanta da jajircewar sabbin shugabannin na nuna alamar cewa za su taka rawa ta kwarai wajen jagoranci da kawo ci gaba mai ma’ana ga reshen Kaduna.

 

REL: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnati Kaduna Jihar Rantsarda

এছাড়াও পড়ুন:

Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC

Sanata Sunday Marshall Katung, wanda ke wakiltar mazabar Kaduna ta Kudu a majalisar dattawa, ya sanar da hukuncin da ya yanke na komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yana mai cewa wannan mataki ne da ya dace domin inganta aikin wakilci da kuma tabbatar da ƙarin haɗin kai ga al’ummar mazabarsa.

A cikin wata sanarwa mai taken “Sabon Babin Rayuwa: Saƙon Haɗin Kai da Manufa Ɗaya,” Sanata Katung ya bayyana cewa wannan shawara ta biyo bayan dogon shawarwari da aka yi da mazauna mazabarsa, jagororin siyasa, iyalansa da abokan aikinsa.

Ya ce, “Wannan sauyin matsayi yana fitowa ne daga niyyar gaskiya ta yin wa mutanenmu hidima cikin inganci, da tabbatar da cewa muryarmu tana da ƙarfi kuma ana jin ta a manyan teburan yanke shawara da ke tsara makomar al’ummarmu.”

Ya ƙara da cewa wannan mataki ya zama dole ne bayan kiraye-kirayen da aka yi daga sassa daban-daban na mazabarsa, tare da yabawa irin sha’awar da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, suka nuna wajen yin aiki tare da shi domin kawo “ci gaba mai tarihi da ban mamaki” a yankin.

Sanata Katung, yayin canza shekan tare da Hon. Daniel Amos da wasu abokansa a Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, ya nuna gamsuwa da “ayukan ci gaban” jam’iyyar APC a yankin Kaduna ta Kudu, yana mai cewa suna nuna adalci, daidaito, da ci gaba.

Ya ce, “Zamanin warewa da nuna bambanci, musamman a baya-bayan nan, yana gushewa, kuma ana maye gurbinsa da gwamnatin da ke da manufa da haɗin kai.”
“Saboda haka muna matsawa gaba domin tabbatar da cewa waɗannan nasarori sun dore kuma sun yadu zuwa sauran al’ummomi da dama a yankin,” in ji shi.

Sanatan ya kuma roƙi abokai da abokan aiki da ba su goyi bayan wannan mataki nasa ba, da su mutunta ra’ayoyi daban-daban, tare da kaucewa barin siyasa ta kawo rarrabuwar kawuna a tsakaninsu.

Ya ambaci kalmar Thomas Jefferson da cewa, “Ban taɓa ɗaukar bambanci a ra’ayi na siyasa, addini ko falsafa a matsayin dalilin janye ƙauna daga aboki ba.”

“A tare, mu ci gaba da zama ɗaya a manufa, mu dage da fata, kuma mu mai da hankali wajen samar da makoma mafi kyau ga al’ummar Mazabar Kaduna ta Kudu.”

Sanata Katung ya tabbatar da ƙudurinsa na ci gaba da aiki don haɗin kai da cigaba.

Daniel Karlmax

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?