Aminiya:
2025-12-09@21:06:54 GMT

Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya yi wata muhimmiyar ganawar sirri da shugabannin sojojin Nijeriya a Abuja ranar Alhamis.

Taron wanda ya gudana daban-daban tare da babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Olatubosun Oluyede da babban hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ikechukwu Ogalla da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hasan Bala Abubakar na shirin sake tura wani sabon yunƙuri na ɗaukar matakin haɗa kai kan maharan Boko Haram.

Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Majiyoyi daga taron sun bayyana cewa, tattaunawar ta ta’allaka ne kan ƙarfafa ayyukan soji a yankin Arewa maso Gabas, da inganta musayar bayanan sirri da magance yawaitar hare-haren da ’yan tada ƙayar baya ke yi a baya-bayan nan.

Gwamna Zulum a ranar Talatar da ta gabata, yayin wani taron tsaro da aka gudanar a Maiduguri, ya koka kan yawaitar hare-haren da ’yan ta’addan ke kai wa a cibiyoyin farar hula da na sojoji, inda ya yi kira da a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki don kaucewa halin da ake ciki.

Zulum ya samu rakiyar Sanatoci masu wakiltar Borno ta Kudu, Mohammed Ali Ndume, Borno ta Arewa Mohammed Tahir Monguno da Borno ta tsakiya Barista Kaka Shehu Lawan.

Sauran a tawagar gwamnan sun haɗa da: Mukhtar Betera Aliyu da Injiniya Bukar Talba, ‘yan majalisar wakilai da Farfesa Usman Tar, kwamishinan yaɗa labarai da tsaron cikin gida na Jihar Borno.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin

Aƙalla sojoji 13 aka cafke a ƙasar Benin bayan yunƙurin da juyin mulki da suka yi bai yi nasara ba.

Majiyoyin tsaro da na soja sun bayyana cewa dukkan waɗanda aka kama sojoji ne masu aiki a halin yanzu, sai mutum ɗaya da ya taɓa yin aiki a rundunar amma ya yi ritaya.

Kama su ta biyo bayan sanarwar da aka yi a talabijin na ƙasar da safiyar Lahadi, inda sojojin suka bayyana cewa sun kifar da gwamnatin Shugaba Patrice Talon tare da rushe dukkan cibiyoyin gwamnati.

Jami’an da suka kira kansu Kwamitin Soja na Sake Tsarawa, sun ce sun karɓe mulki, sun rufe iyakokin ƙasar tare da dakatar da jam’iyyun siyasa.

Sai dai fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da cewa Shugaba Talon yana cikin ƙoshin lafiya, kuma dakarun da suka tsaya kan gaskiya na dawo da doka da oda.

Gwamnati ta bayyana lamarin a matsayin aikin “tsiraru  mutane” da ba su da tasiri.

“Wasu ’yan tsiraru ne kawai da ya mamaye talabijin. Rundunar sojan ƙasa na sake karɓar iko. Birnin da ƙasar gaba ɗaya suna cikin tsaro,” in ji sanarwar fadar shugaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Ya Yi Wani  Hatsari a Neja
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin