Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji
Published: 11th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya yi wata muhimmiyar ganawar sirri da shugabannin sojojin Nijeriya a Abuja ranar Alhamis.
Taron wanda ya gudana daban-daban tare da babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Olatubosun Oluyede da babban hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ikechukwu Ogalla da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hasan Bala Abubakar na shirin sake tura wani sabon yunƙuri na ɗaukar matakin haɗa kai kan maharan Boko Haram.
Majiyoyi daga taron sun bayyana cewa, tattaunawar ta ta’allaka ne kan ƙarfafa ayyukan soji a yankin Arewa maso Gabas, da inganta musayar bayanan sirri da magance yawaitar hare-haren da ’yan tada ƙayar baya ke yi a baya-bayan nan.
Gwamna Zulum a ranar Talatar da ta gabata, yayin wani taron tsaro da aka gudanar a Maiduguri, ya koka kan yawaitar hare-haren da ’yan ta’addan ke kai wa a cibiyoyin farar hula da na sojoji, inda ya yi kira da a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki don kaucewa halin da ake ciki.
Zulum ya samu rakiyar Sanatoci masu wakiltar Borno ta Kudu, Mohammed Ali Ndume, Borno ta Arewa Mohammed Tahir Monguno da Borno ta tsakiya Barista Kaka Shehu Lawan.
Sauran a tawagar gwamnan sun haɗa da: Mukhtar Betera Aliyu da Injiniya Bukar Talba, ‘yan majalisar wakilai da Farfesa Usman Tar, kwamishinan yaɗa labarai da tsaron cikin gida na Jihar Borno.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI
Babban sakataren kungiyar Hezbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’em Qasim ya godewa shugabancin JMI, wato Imam Sayyif Aliyul Khaminaei kan goyon bayan da yake bawa kungiyar babu kakkautawa don yakar makiyar kasar HKI.
Shugaban kungiyar ya bayyana haka ne a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta kasar Lebanon, a karon farko tun bayan shahadr shugaban kungiyar Sayyid Hassan Nasarallah a shekarar da ta gabata.
Babban malamin ya kara da cewa, taimakon da Imam Khaminae yayiwa kungiyar Hizbullah, ya kai matsayinda ba zamu tambaya, ko roka ba. Musamman bayan fara yaki a cikin watan Octoban shekara ta 2023, kuma ta bada wadannan taimakon ba tare da ta shiga yakin kai tsaye ba.
Sheikh Qasem ya bayyana cewa, bamu bukaci JMI ta shiga yakin ba, kuma bai kamata ta shiga yakin ba, saboda muma bama bukatar da shiga yakin.
Daga karshen shugaban kungiyar ya bayyana cewa zancen da aka cika duniya da shin a cewa kungiyar ta mika makamanta ga gwamnatin kasar. Saboda takurawar da manya-manyan kasashen duniya suke yi don shi ne bukatar HKI.
Don haka yamata su san cewa bamu da Kalmar mika kai a kamusimmu, ko nasara ko shahada babu wata na uku iji shi.
Kuma wannan halin da ake ciki, na keta hurimun yarjeniyar 1701 wanda HKI take yi ba zai dore har’abada ba.