Aminiya:
2025-11-27@05:57:37 GMT

Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya yi wata muhimmiyar ganawar sirri da shugabannin sojojin Nijeriya a Abuja ranar Alhamis.

Taron wanda ya gudana daban-daban tare da babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Olatubosun Oluyede da babban hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ikechukwu Ogalla da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hasan Bala Abubakar na shirin sake tura wani sabon yunƙuri na ɗaukar matakin haɗa kai kan maharan Boko Haram.

Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Majiyoyi daga taron sun bayyana cewa, tattaunawar ta ta’allaka ne kan ƙarfafa ayyukan soji a yankin Arewa maso Gabas, da inganta musayar bayanan sirri da magance yawaitar hare-haren da ’yan tada ƙayar baya ke yi a baya-bayan nan.

Gwamna Zulum a ranar Talatar da ta gabata, yayin wani taron tsaro da aka gudanar a Maiduguri, ya koka kan yawaitar hare-haren da ’yan ta’addan ke kai wa a cibiyoyin farar hula da na sojoji, inda ya yi kira da a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki don kaucewa halin da ake ciki.

Zulum ya samu rakiyar Sanatoci masu wakiltar Borno ta Kudu, Mohammed Ali Ndume, Borno ta Arewa Mohammed Tahir Monguno da Borno ta tsakiya Barista Kaka Shehu Lawan.

Sauran a tawagar gwamnan sun haɗa da: Mukhtar Betera Aliyu da Injiniya Bukar Talba, ‘yan majalisar wakilai da Farfesa Usman Tar, kwamishinan yaɗa labarai da tsaron cikin gida na Jihar Borno.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere

Yundunar ’Yan Sandan Jihar Borno ta tabbatar da cewa ɗaya daga cikin ’yan mata 14 da ƙungiyar ISWAP ta sace a Ƙaramar Hukumar Askira-Uba ta kuɓuta, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano sauran 13.

A sanarwar da ya fitar dangane da irin ƙoƙarin da Jami’an tsaron ke yi na ceto sauran ‘yan matan 13 da ke hannun ‘yan ta’addan, kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce, shugaban gundumar Huyum ya bayar da rahoto a ranar Asabar 22 ga Nuwamba cewa waxanda ake zargin mayaƙan Ƙungiyar ISWAP ne suka sace ‘yan matan, yayin da suke aiki a wata gona a gundumar Mussa.

Tawagar ’yan sanda, sojoji, Sibiliyan JTF, da mafarauta da ’yan banga nan da nan suka fara aikin bincike don ceto ’yan matan.

“Ɗaya daga cikin waxanda abin ya shafa ta tsira ba tare da wata matsala ba a lokacin aikin kuma an ceto ta,” in ji Daso.

Mayaƙan Boko Haram sun file kan mata 2 a Borno Sace ɗalibai: Idan ba zai iya ba ya sauka kawai— PDP

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Naziru Abdulmajid, ya yi kira ga mazauna yankin da su kasance masu lura yayin da hukumomin tsaro ke ƙara himma wajen ƙoƙarin ceto sauran ‘yan matan.

Sanarwar ta ce, “Ana shawartar manoma da mazauna yankin da su yi aiki a yankunan da jami’an tsaro ke sintiri,” in ji sanarwar.

Rundunar ta ce za a samar da ƙarin bayani yayin da ake ci gaba da aikin gano wurin da waɗannan mata suke.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe
  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana