HausaTv:
2025-12-04@00:38:58 GMT

Trump ya janye harajin da ya kara wa duniya, amma ya laftawa China 125%

Published: 10th, April 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da haraje-harajen da ya lafta kan kayayyakin da ke shiga kasar daga kasashen duniya, sai dai ya kara harajin da kashi 125 ga kasar China.

A wani bayani da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Shugaba Trump ya ce za a rage haraje-harajen zuwa kashi 10%, sai dai za a kara wanda aka lafta kan kayan China zuwa kashi 125%.

Donald Trump ya kuma zargi China da nuna rashin girmamawa da kuma zaluntar Amurka.

Kafin haka, China ta sanar da kara haraji kan kayan Amurka da ake shiga da su kasarta zuwa kashi 84% – inda Chinar ta zargi Amurka da barazana kan kasashen duniya.

Matakin na zuwa ne jim kadan bayan da Beijing ta mayar da martani ga karin harajin da Washington ta yi a baya

Trump ya kuma yi nuni da cewa, ba kamar China ba, “wadannan kasashen, bisa ga kwakkwarar shawarata, ba su mayar da martani ta kowace hanya, ko siffa, a kan Amurka ba.”

Kazalika, jami’an Amurka sun bayyana a wannan rana cewa, yanzu kasashe ko kungiyoyin kasa da kasa fiye da 50 sun riga sun tuntubi Amurka kan matakin nata na harajin kwastam.

Wannan lamarin ya shafi kasashe 70 na duniya, wani abu da ya haddasa barkewar rikicin kasuwanci tsakanin Amurkar da kasashe da dama, musamman manyan kasashen da take huldar kasuwanci da su, kamar China da kuma kasashen Tarayyar Turai.

Su ma kasashen Tarayyar Turai sun lafta harajin kashi 25 cikin dari kan kayan da Amurka da ake shiga da su yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran

Rahotanni sun bayyana cewa ministan harkokin wajen kasar Turkiya ya iso birnin Tehran a jiya lahadi kuma  ya samu kyakkyawar tarba daga takwaransa na kasar iran Abbas Araqchi.

Ziyarar tasa ana saran za ta kara fadada dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, ganin cewa dukkan kasashen biyu suna taka rawa a batutun da suka shafi yanki dama duniya baki daya.

Bugu da kari bayan ganawarsa da Araqchi da musayar ra’ayoyi kan batutuwa daban daban, zai gana da sauran manyan jami’an gwammnatin kasar, da ake saran za su tattauna kan alakar dake tsakaninsu da kuma irin ci gaban da aka samu a yankin da dai sauran batutuwa na kasa da kasa.

Ana sa bangaren shugaban kasar iran Masud pezeshkiyan a lokacin ganawarsa da Hakan fidan ministan harkokin wajen kasar turkiya ya jaddada game da muhimmancin hadin kan kasashen musulmi cikin gaggawa, yace ya kamata kasashen musulmi su rike duba yanayi da yan uwansu suke ciki, kuma a nisanci tsaurara alamura, adaidai lokacin da suke fuskantar matsin lamba daga kasashen waje.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi December 1, 2025 Shugaban Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban  “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025  Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Turkiya November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10
  • Jagoran ‘Yan Democrat a Majalisar Dattawa: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela
  • Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran