HausaTv:
2025-11-07@18:52:26 GMT

 Rasha Ta Sanar Da Kakkabo Da Jirage Marasa Matuki 57 Da Ukiraniya Ta Harba

Published: 19th, March 2025 GMT

Ma’aikatar tsaron kasar Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki 57 da kasar Ukiraniya ta harba zuwa yankuna mabanbanta na kasar.

A yau Laraba ne ma’aikatar tsaron kasar ta Rasha ta sanar da cewa; An harbo jiragen marasa matuki 35 da aka harba wa yankin Kursk dake yammacin Syria a jiya da dare.

Sai kuma wasu jiragen 13 da aka harba a yankin Oryol da kuma wasu 7 a samaniyar tekun Azorf. Sauran yankunan da sojojin Ukuraniya su ka harba wa makamai masu linzamin sun hada  Tola, da Biryansk.

Kwanaki biyu da su ka gabaa ma dai sojojin na Rasha sun sanar da kakkabo wasu jirage marasa matuki na Kasar Ukiraniya 31 da aka harba a yankuna mabanbanta na kasar.

 A gefe daya sojojin na kasar Ukiraniya sun kai wasu hare-hare akan garuruwan da suke kan iyaka da Rasha, da su ka hada garuruwan Zawalishnika da Korsta.

Majiyar  tsaron Rasha ta ce, sun kashe sojojin Ukiraniya 220 a cikin sa’oi 24.

A gefe daya Amurka ta sanar da cewa a ranar Lahadi mai zuwa za a bude tattaunawa a tsakanin Rasha da Amurka a birnin Jidda na kasar Saudiyya.

Manzon musamman na Amurka Steve Vitcov ya bayyana cewa,tattaunawar za ta mayar da hankali ne akan yadda za a kawo karshen yakin kasar Ukiraniya.

A jiya Talata an yi tattaunawa ta wayar tarho a tsakanin shugabannin kasashen Rasha da na Amurka akan batun kasar ta Ukiraniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Ukiraniya ta sanar da

এছাড়াও পড়ুন:

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

“A yayin da ake tarwatsa masu kai harin, DPO na Sassan A da B sun tura ma’aikatansu suka harba hayaki mai sa hawaye, amma wasu motoci cikin motar gwamnan sun lalace,” in ji Abiodun.

Ya bayyana cewa mutane uku na farko da ake zargi sune Ali Mohammed da Adamu Hussain, dukkansu daga yankin Nasarafu, Bida, da Isah Umaru na yankin Darachita, Bida. Ya kara da cewa an kama Nagenu, mai shekaru 39, daga yankin Bello Masaba, daga baya dangane da wannan lamari, sannan ya ambaci wasu biyu, Salihu Mohammed da Abdulrahman Baba, yayin tambayoyi.

“Dukkan wadanda ake zargi suna karkashin bincike kuma suna taimaka wa ‘yansanda wajen gano wasu. Ana ci gaba da kokarin kama karin mutane da ake zargi,” in ji Abiodun.

Lauyan Nagenu, Barrister Ibrahim Wali, ya kuma tabbatar da kama abokin aikinsa ga *Daily Trust*, yana cewa ana tsare da shi a Ofishin Rundunar ‘Yan Sanda na Yanki a Bida. Ya bayyana cewa kama shi na da alaka da bidiyon da ya bazu, kuma ana daukar matakan shari’a don samun ‘yancinsa.

Kokarin tuntubar jami’an NNPP bai samu nasara ba. Kiran da aka yi ga shugaban jam’iyyar na jihar, Danladi Umar Abdulhamid, bai yi nasara ba, kuma bai amsa sakonnin da aka tura masa ba.

Gwamnatin Neja ta yi alkawarin gurfanar da masu laifi a gaban shari’a

Babban Mataimakin Musamman ga Gwamna kan Tattara Matasa, Hamza Bida, ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar an hukunta wadanda suka yi wannan hari.

Yayin da yake magana da Daza TB, wata kafar yada labar ta Hausa, ya ce wannan lamari ba shi da alaka da zaben kananan hukumomi.

“Ban ji dadi da abin da wadannan yara suka yi a Bida ba. Abin da ya faru shi ne, a rana daya kafin zaben, mutane sun taru a gidan gwamna kuma ya yi musu alkawarin ba su kudi a ranar Lahadi. Daga baya daren nan, an kafa wani kwamitin, ciki har da dan majalisar wakilai na Bida/Gbako/Katcha, don tabbatar da cewa kudin ya isa ga kowa,” in ji Bida.

Ya kara da cewa wasu matasa, wadanda ba su gamsu da tsarin ba, suka rikide zuwa tashin hankali. “Wadanda suka yi wannan aikatawa yara ne da iyayensu suka rasa ikon kula da su, amma za mu koya musu darasi,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki November 7, 2025 Labarai Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja November 7, 2025 Manyan Labarai Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah November 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku a Kudancin Lebanon  
  • Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Kwamitin Gwamnonin IAEA
  • Hamas Ta yi Watsi Da Batun Tura Sojojin Kasashen Waje Zuwa Gaza
  • Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar