Rasha Ta Sanar Da Kakkabo Da Jirage Marasa Matuki 57 Da Ukiraniya Ta Harba
Published: 19th, March 2025 GMT
Ma’aikatar tsaron kasar Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki 57 da kasar Ukiraniya ta harba zuwa yankuna mabanbanta na kasar.
A yau Laraba ne ma’aikatar tsaron kasar ta Rasha ta sanar da cewa; An harbo jiragen marasa matuki 35 da aka harba wa yankin Kursk dake yammacin Syria a jiya da dare.
Kwanaki biyu da su ka gabaa ma dai sojojin na Rasha sun sanar da kakkabo wasu jirage marasa matuki na Kasar Ukiraniya 31 da aka harba a yankuna mabanbanta na kasar.
A gefe daya sojojin na kasar Ukiraniya sun kai wasu hare-hare akan garuruwan da suke kan iyaka da Rasha, da su ka hada garuruwan Zawalishnika da Korsta.
Majiyar tsaron Rasha ta ce, sun kashe sojojin Ukiraniya 220 a cikin sa’oi 24.
A gefe daya Amurka ta sanar da cewa a ranar Lahadi mai zuwa za a bude tattaunawa a tsakanin Rasha da Amurka a birnin Jidda na kasar Saudiyya.
Manzon musamman na Amurka Steve Vitcov ya bayyana cewa,tattaunawar za ta mayar da hankali ne akan yadda za a kawo karshen yakin kasar Ukiraniya.
A jiya Talata an yi tattaunawa ta wayar tarho a tsakanin shugabannin kasashen Rasha da na Amurka akan batun kasar ta Ukiraniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Ukiraniya ta sanar da
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
Dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ya bayyana cewa makamai masu linzamu na dakarun sun fada kan matatar man fetur na Haifa a HKI har sau biyu a yakin kwanaki 12 da ta fafata da Iran a cikin watan Yunin wannan shekara.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Burgediya Janar Ali Mohammad Naeini kakakin dakarun ya na fadar haka a jiya Lahadi a wani taro, ya kuma kara da cewa makaman har’ila yau sun kashe jami’an hukumar leken asirin HKI MOSAD har 36 a wani hari kan ginin hukumar a cikin yakin.
Naeini, ya kara da cewa HKI ta yi kuskuren lissafi a lokacinda ta farwa kasar Iran da yaki a cikin watan Yunin da ya gabata, tare da tsammanin cewa JMI ba zata iya maida martani ba, saboda rauni, don an kashe manya-manyan kwamandojin sojojin kasar sannan ba zata iya amfani da makamanta na kare dangi ba.
A ranar 13 ga watan Yuni na wannan shekara ne HKI tare da Amurka suka farwa kasar Iran da yaki, da nufin kifar da gwamnatin kasar da kuma kawo karshen shirinta na makamashin nukliya kwata-kwata. Saboda haka ne jiragen yakin Amurka samfurin B2 suka kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin Nukliya na kasar dake Fordo, Natanz da kuma Esfahan.
Naeni ya cewa Iran ta cilla makamai masu linzami har 14 kan sansanin sojojin Amurka mafi girma na Al-Udaid da ke kasar Qatar, sannan yace bisa lissafin Amurkawa kan su sun kashe dalar Amurka miliyon 111 wajen bibiyan inda makaman iran zasu fada.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025 Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro December 8, 2025 Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka Teke Fuskanta December 8, 2025 Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci