Rasha Ta Sanar Da Kakkabo Da Jirage Marasa Matuki 57 Da Ukiraniya Ta Harba
Published: 19th, March 2025 GMT
Ma’aikatar tsaron kasar Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki 57 da kasar Ukiraniya ta harba zuwa yankuna mabanbanta na kasar.
A yau Laraba ne ma’aikatar tsaron kasar ta Rasha ta sanar da cewa; An harbo jiragen marasa matuki 35 da aka harba wa yankin Kursk dake yammacin Syria a jiya da dare.
Kwanaki biyu da su ka gabaa ma dai sojojin na Rasha sun sanar da kakkabo wasu jirage marasa matuki na Kasar Ukiraniya 31 da aka harba a yankuna mabanbanta na kasar.
A gefe daya sojojin na kasar Ukiraniya sun kai wasu hare-hare akan garuruwan da suke kan iyaka da Rasha, da su ka hada garuruwan Zawalishnika da Korsta.
Majiyar tsaron Rasha ta ce, sun kashe sojojin Ukiraniya 220 a cikin sa’oi 24.
A gefe daya Amurka ta sanar da cewa a ranar Lahadi mai zuwa za a bude tattaunawa a tsakanin Rasha da Amurka a birnin Jidda na kasar Saudiyya.
Manzon musamman na Amurka Steve Vitcov ya bayyana cewa,tattaunawar za ta mayar da hankali ne akan yadda za a kawo karshen yakin kasar Ukiraniya.
A jiya Talata an yi tattaunawa ta wayar tarho a tsakanin shugabannin kasashen Rasha da na Amurka akan batun kasar ta Ukiraniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Ukiraniya ta sanar da
এছাড়াও পড়ুন:
DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.
Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.
NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Ukuwannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.
Domin sauke shirin, latsa nan