Rasha Ta Sanar Da Kakkabo Da Jirage Marasa Matuki 57 Da Ukiraniya Ta Harba
Published: 19th, March 2025 GMT
Ma’aikatar tsaron kasar Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki 57 da kasar Ukiraniya ta harba zuwa yankuna mabanbanta na kasar.
A yau Laraba ne ma’aikatar tsaron kasar ta Rasha ta sanar da cewa; An harbo jiragen marasa matuki 35 da aka harba wa yankin Kursk dake yammacin Syria a jiya da dare.
Kwanaki biyu da su ka gabaa ma dai sojojin na Rasha sun sanar da kakkabo wasu jirage marasa matuki na Kasar Ukiraniya 31 da aka harba a yankuna mabanbanta na kasar.
A gefe daya sojojin na kasar Ukiraniya sun kai wasu hare-hare akan garuruwan da suke kan iyaka da Rasha, da su ka hada garuruwan Zawalishnika da Korsta.
Majiyar tsaron Rasha ta ce, sun kashe sojojin Ukiraniya 220 a cikin sa’oi 24.
A gefe daya Amurka ta sanar da cewa a ranar Lahadi mai zuwa za a bude tattaunawa a tsakanin Rasha da Amurka a birnin Jidda na kasar Saudiyya.
Manzon musamman na Amurka Steve Vitcov ya bayyana cewa,tattaunawar za ta mayar da hankali ne akan yadda za a kawo karshen yakin kasar Ukiraniya.
A jiya Talata an yi tattaunawa ta wayar tarho a tsakanin shugabannin kasashen Rasha da na Amurka akan batun kasar ta Ukiraniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Ukiraniya ta sanar da
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta sanar da cewa tana sake duba dangantakarta da Tanzania a daidai lokacin da ake samun abin da Amurka ta kira damuwa game da ‘yancin addini, ‘yancin fadin albarkacin baki, cikas ga ayyukan zuba hannayen jarin Amurka, da kuma cin zarafin fararen hula.
Amurka ta bayar da gargadin tsaro ga Amurkawa a kasar da ke Gabashin Afirka bayan babban zaben watan Oktoba, wanda zanga-zangar ta mamaye shi.
Kungiyoyin kare hakkin dan adam, jam’iyyun adawa, da Majalisar Dinkin Duniya sun bayar da rahoton cewa an samu matsaloli bayan zaben, duk da cewa dai gwamnatin kasar ta musanta alkaluma na asarorin da aka samu, tana mai kiransu da alkalumman karin gishiri.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce kasar na gudanar da cikakkiyar bita bayan matakan da gwamnatin Tanzania ta dauka kwanan nan sun haifar da damuwa sosai game da dangantakar kasashen biyu da kuma amincin dake tsakaninsu a matsayin abokan tarayya.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fada a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis cewa “ci gaba da danne ‘yancin addini da ‘yancin fadin albarkacin baki, ci gaba da kawo cikas ga zuba jarin Amurka, da kuma tashin hankali mai ban tsoro da ya fara tun kafin zaben ranar 29 ga Oktoba a Tanzania ya haifar da yanayin da yasa dole ne Amurka ta sake duba dangantakarsu.” A cewar bayanin ma’aikatar harkokin wajen Amurka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale December 4, 2025 Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon December 4, 2025 An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila December 4, 2025 An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya December 4, 2025 Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata December 4, 2025 Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe December 4, 2025 MDD ta nemi a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma Tuddan Golan December 4, 2025 Rundunar Ruwa ta IRGC na Gudanar Da Atisayen Soja a Tekun Fasha December 4, 2025 Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya December 4, 2025 Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Gaza December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci