Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen
Published: 16th, March 2025 GMT
Kungiyar Hizbullah ta yi Allah wadai da harin da Amurka da Birtaniya suka kai kan kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da dama a daren jiya Asabar.
Kungiyar Hizbullah ta yi Allah wadai da wadannan hare-haren wuce gona da iri da Amurka da Birtaniya suka kai kan wasu unguwanni a Sanaa babban birnin kasar, da kuma wasu larduna da dama, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba.
Bayanin ya kara da cewa, “Wannan zaluncin ya zo ne a matsayin wani yunkuri na murkushe wannan al’umma mai girma mai tsayin daka wajen ci gaba da nuna goyon bayanta ga al’ummar Gaza da kuma ci gaba da nuna goyon baya ga al’ummar Palasdinu.”
Sanarwar ta yi nuni da cewa, hare-haren da ake kaiwa fararen hula da muhimman ababen more rayuwa a kasar Yaman, ya sake bayyana hakikanin gaskiya da mummunar fuskar gwamnatin Amurka, wadda ke aiwatar da ayyukan cin zarafi ga kasashen da ke adawa da manufofinta a yankin da ma duniya baki daya.
Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta bayyana harin da Amurka ta kai birnin San’a a matsayin laifin yaki da kuma keta dokokin kasa da kasa, wanda kuma ya yi dai-dai da irin hare-haren Isra’ila a kan Gaza, Siriya, kuma Lebanon.
Hizbullah ta ci gaba da cewa: Al’ummar kasar Yemen masu tsayin daka, wadanda suka rubuta kasidu na jarumtaka tare da jinin shahidansu na goyon bayan al’ummar Palastinu da Gaza, kuma suka tsaya tsayin daka a karkashin jajircewar shugabanninsu, irin wannan al’umma ba za su ja da baya ba wajen tinkarar wannan zalunci na makiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce: An Rusa Gaza Gaba Daya
Jami’in Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Ruguza Gaza “ba abin da za a gaskata ba ne” domin an rusa yankin gaba daya
Mataimakin babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya mai kula da harkokin jin kai, Tom Fletcher, ya ce: Girman barnar da aka yi a zirin Gaza abu ne da ba za a taba mantawa da shi ba, yana mai jaddada cewa, “an ruguza komai tare da mai da yankin baraguzai,” yana mai nuni da irin barnar da aka yi wa ababen more rayuwa, da gidaje, da kashe fararen hula.
A cikin wata sanarwa ga gidan talabijin na Al Jazeera, Fletcher ya nuna cewa an riga an fara shirin ba da agajin jin kai na kwanaki 60. Shiri ne mai girma, wanda kashi na farko ke da nufin sauƙaƙe shigar da kayan agaji mai mahimmanci a cikin yankin.
Ya bayyana cewa, “Tsarin ya hada da samar da biredi, kawo tantuna, da inganta ayyukan tsaftar muhalli, baya ga kokarin dawo da asibitoci da makarantu, ganin yadda bangaren lafiya da ilimi ke fuskantar durkushewa.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Joseph Kabila Ya Koma Kasarsa Domin Kalubalantar Hukuncin Kisa Da Aka Yanke Kansa October 18, 2025 Gaza Ta Bukaci A Binciki Isra’ila Kan Sace Sassan Jiki A Gawarwakin Falasdinawa October 18, 2025 Hamas Ta Bukaci A Kafa Kotun Kasa Da Kasa Kan Gawarwarkin Da Isra’ila Ta Dawo Mata Da Su. October 18, 2025 Madagascar : An rantsar Da Michael Randrianirina A Matsayin Shugaban Kasar October 18, 2025 Iran Ta yi Tir Da Harin da Isra’ila Ta kai Kudancin Kasar labanon. October 18, 2025 Majalisar Dattawa Za Ta Gana Da Ministan Ilimi Kan Batun Yajin Aikin Asuu. October 18, 2025 Gaza ta bukaci a binciki Isra’ila kan sace sassan jiki a gawarwakin falasdinawa October 18, 2025 Madagaska : An rantsar da Kanar Randrianirina a matsayin shugaban kasa October 18, 2025 Al-Houthi: Matsin lamba bai hana Iran ci gaba da goyon bayan Falasdinu ba October 18, 2025 Marzieh Jafari Ta Dauki Lambar Yabo Ta Horar Da Mata Wasan Kwallon Kafa Ta Nahiyar Asia October 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci