HausaTv:
2025-07-12@08:22:12 GMT

Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen

Published: 16th, March 2025 GMT

Kungiyar Hizbullah ta yi Allah wadai da harin da Amurka da Birtaniya suka kai kan kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da dama a daren jiya Asabar.

Kungiyar Hizbullah ta yi Allah wadai da wadannan hare-haren wuce gona da iri da Amurka da Birtaniya suka kai kan wasu unguwanni a Sanaa babban birnin kasar, da kuma wasu larduna da dama, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba.

Bayanin ya kara da cewa, “Wannan zaluncin ya zo ne a matsayin wani yunkuri na murkushe wannan al’umma mai girma mai tsayin daka wajen ci gaba da nuna goyon bayanta ga al’ummar Gaza da kuma ci gaba da nuna goyon baya ga al’ummar Palasdinu.”

Sanarwar ta yi nuni da cewa, hare-haren da ake kaiwa fararen hula da muhimman ababen more rayuwa a kasar Yaman, ya sake bayyana hakikanin gaskiya da mummunar fuskar gwamnatin Amurka, wadda ke aiwatar da ayyukan cin zarafi ga kasashen da ke adawa da manufofinta a yankin da ma duniya baki daya.

Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta bayyana harin da Amurka ta kai birnin San’a a matsayin laifin yaki da kuma keta dokokin kasa da kasa, wanda kuma ya yi dai-dai da irin hare-haren Isra’ila a kan Gaza, Siriya, kuma Lebanon.

 Hizbullah ta ci gaba da cewa: Al’ummar kasar Yemen masu tsayin daka, wadanda suka rubuta kasidu na jarumtaka tare da jinin shahidansu na goyon bayan al’ummar Palastinu da Gaza, kuma suka tsaya tsayin daka a karkashin jajircewar  shugabanninsu, irin wannan al’umma ba za su ja da baya ba wajen tinkarar wannan zalunci na makiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
  • Associated Press: Harin Iran Akan Sansanin Amurka Dake Kasar Qatar Ya Lalata Wata Cibiyar Sadarwa
  • HKI Ta Roki Amurka Ta Taimake Ta A Fada Da Kasar Yemen
  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Mayakan Huthi Sun Kara Kai Wasu Hare-Hare da Makamai Masu Linzami Kan BenGurio
  • HKI Ta Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Kudancin Kasar Lebanon
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • Kazem Sajjadpour Ya ce: Iraniyawa Suna Daukan Tarayyar Turai Ma Goyon Bayan Harin Zaluncin Isra’ila Kansu