“ Zuba hannun jari a bangaren da ake sauke kaya a Tashohin Jiragen Ruwa da kara fadada hanyoyin layin Jiragen kasa, za su iya taimakawa wajen bunkasa aiki da kuma kara sanya gasa a ayyukan tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwa. A cewar Dantsoho
Ya sanar da cewa, samar da kyakaywan yanayin kasuwanci a kasar nan na da alaka da kokari da kuma yanayin gasar da aka samar na kasa a Tashishin Jiragen Ruwan, inda ya yi nuni da cewa, wadannan abubuwan sun taimaka wajen samun musayar kudade, daidaita tattalin ardikin kasar, kara habaka kauswanci da kuma samun masu zuwa zuba hannun jari.

Dantsoho ya godewa Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Ruwa Adegboyega Oyetola, bisa goyon bayan ada yake ci gaba da bai wa Hukumar, musamman domin a kara saita Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

Ya yi nuni da cewa, hadakar da NPA ta yi da Kungiyar kasa da kasa ta IMO za ta taimaka wajen cimma burin wannan aikin da aka sanya a gaba.

Da yake yin tsokaci kan tsarin zamanai da Hukumar ta kirkiro da shi na shigar manyan motoci cikin Tashoshin Jaregn Ruwan kasar Shugaban ya bayyana cewa, akwai hadaka a tsakanin aikin da ake gudanarwa a Tashar Jiragen Ruwa da kuma wanda ake gudanarwa a a wajen kwashe kayana da aka shigo da su ta Tashoshin Jiragen Ruwa.

A cewarsa, ana yin hakan ne, musamman domin a tabbatar da na rage cunkoso a cikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, wanda hakan ya sanya Hukumar ta janyo kamfanin Messrs, domin gudanar da wannan aikin.
Ya sanar da cewa, ya zuwa yanzu sama da manyan motoci 70,000 ne, suka yi rijista da wannan kamfanin na Messrs.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje

Mai magana da yawun hukumar da take kula da filin saukar jiragen sama ta Ben Gorion ta sanar a yau Asabar cewa an rufe filin saukar jiragen saman har zuwa wani lokaci a nan gaba, bayan da aka dauke dukkanin jiragen sama zuwa kasashen Cyprus, Greece da kuma Amurka.

Mai Magana da yawun hukumar filin saukar jiragen saman na Ben Gorion  Lisa Daiper ta bayyana ce; Babu wani lokaci takamaimai da aka tsayar domin sake bude filin saukar jiragen saman na Ben Gorion.”

 A gefe daya jaridar “Maariv’ ta bayyana cewa; An dauke dukkanin jiragen sama zuwa filayen  jiragen saman a kasashen turai.

Haka nan kuma ta kara da cewa; An dauki 14 daga cikin jiragen saman na HKI zuwa filin saukar jiragen saman a Laranka da Papus dake tsibirin Cyprus da su ne filayen jiragen sama na nahiyar turai mafi kusa da HKI.

Su kuwa jiragen da shugabannin ‘yan sahayoniya suke shiga an kai su ne zuwa filin jirgin sana na birnin Athenia na kasar Girka, wasu kuwa zuwa kasashen Bulgari da Faransa.

Dauke jiragen na ‘yan sahayoniya dai ya zo ne saboda tsoron kar makamai masu linzami na Iran su isa gare su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi