Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
Published: 15th, March 2025 GMT
Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada sanarwan cewa a shirye take da saki fursinonin HKI da Amurka, har ma da gawakin wasu 4, idan HKI ta dawo kan ci gaba da aiwatar da abubuwan da yarjeniyar tsagaita wuta a tsakaninta da HKI.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wani Jami’in kungiyar yana fadar haka a jiya Jumma’a.
Taher al-Nounou ya fadawa kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa kan cewa Hamas zata salami Edan Alexander wanda yake dauke da passport na Amurka da kuma wasu 4 wadanda suke dauke da Passport na kasashen biyu wato HKI da kuma Amurka. Amma tare da wannan sharadin.
Sanarwan ta kammala da cewa kungiyar ta fara sabuwar tattaunawa a birnin Doha na kasar Qatar a ranar Talatan da ta gabata sannan tawagar HKI ma tana halattar tattaunawan wand aba kai tsaye ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Gwamnonin Jihohi Ta Jajintawa Jihar Adamawa Bisa Ambaliyar Ruwa A Yola
Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) kuma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana alhinin sa kan rahotannin ambaliya mai tsanani da ta faru a Yola, Jihar Adamawa, wacce ta yi sanadiyar mutuwar mutane, da asarar dukiyoyi da kuma raba dimbin jama’a da muhallansu.
A cikin wata sanarwa, Gwamna AbdulRazaq ya ce kungiyar NGF na jajantawa gwamnatin Jihar Adamawa ƙarƙashin jagorancin Mai Girma Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri yayin da suke kokarin tara kayan agaji da daukar matakan rage illar wannan iftila’in.
Sanarwar ta kara da cewa, kungiyar ta yaba da matakin gaggawa da ‘yan sanda da kuma dakarun sojin Najeriya suka dauka na tura rundunonin ruwa, bisa gayyatar gwamnatin jihar, domin taimaka wa al’ummar da abin ya shafa a wannan lokaci na halin kaka-ni-ka-yi.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa kungiyar za ta bayar da nata tallafin domin taimakawa al’ummar jihar bisa halin da suka tsinci kansu a ciki.
Ali Muhammad Rabi’u