Aminiya:
2025-06-15@20:05:34 GMT

’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja

Published: 13th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga, Salisu Mohammed, wanda aka fi sani da Dogo Saleh, a wani artabu da suka yi da shi a dajin Gidan-Abe da ke kan iyakar Bwari da Kaduna.

Sun samu nasarar ne bayan samun bayanan sirri kan shigowar ‘yan bindiga yankin daga Kaduna.

NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

Kwamishinan ’Yan Sandan Abuja, Olatunji Rilwan Disu, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce jami’an rundunar yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin Mustapha Muhammed, sun tare hanyar ’yan bindigar, inda suka yi musayar wuta da su.

“Mun yi nasarar kawar da barazana babba da ke addabar al’umma da hanyoyi,” in ji Disu.

An gano cewa Mohammed, mai shekaru 21, yana ɗaya daga cikin manyan ’yan bindigar da ke aiki a dajin Rijana na Kaduna.

“Ya sace mutane da yawa, ciki har da kashe jami’an tsaro da fararen hula.

“Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar AK-49, harsasai 60, da kuma Naira miliyan uku, da ake zargin kuɗin fansa ne da suka samu daga garkuwa da mutane,” in ji shi.

Bincike ya tabbatar da cewa ɗan bindigar na da hannu a kai hare-hare kauyukan Kike da Bagada, inda ya jagoranci garkuwa da mutane tare da karɓar kuɗin fansa.

“Ayyukansa sun jefa jama’a cikin fargaba, amma jami’anmu sun aika da saƙo mai ƙarfi cewa ba za a lamunci aikata laifi ba,” in ji Disu.

Wani jami’in ’yan sanda ya samu rauni kaɗan a yayin artabun, amma an ba shi kulawar da ya dace, inda yake murmurewa.

A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da farautar sauran ‘yan bindigar da suka tsere tare da rushe duk wani sansanin ’yan bindiga da ke iyakar Abuja da Kaduna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari Ƙasurgumin Ɗan Bindiga musayar wuta yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

Wasu mazauna Jihar Katsina sun yi zaman sulhu da wasu shugabannin ’yan daban daji da suka addabe su.

Wakilinmu ya ruwaito cewa an yi taron sasanci da ’yan bindigar daji ne a Ƙaramar Hukumar Danmusa, wanda rundunar sojoji ke shiryawa, inda Adamu Aliero ya jagoranci sashen ’yan bindigar.

BBC ya ruwaito Kwamishinan Tsaro da Harkokin Ciki Gida na Katsina na cewa al’ummar garin Bicci da ke yankin Ƙaramar Hukumar Danmusa sun zauna tare da Ado Aliero da sauran wasu shugabannin ’yan bindigar aƙalla goma.

“An zauna da Ado Aliero da Kamilu Buzaru da Dogo Nahali da Wada Jargaba da Dahiru Buzu haka ma da Nagoggo,” in ji shi.

Hotuna daga Ahmed Kabiru S/Kuka

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara