’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja
Published: 13th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga, Salisu Mohammed, wanda aka fi sani da Dogo Saleh, a wani artabu da suka yi da shi a dajin Gidan-Abe da ke kan iyakar Bwari da Kaduna.
Sun samu nasarar ne bayan samun bayanan sirri kan shigowar ‘yan bindiga yankin daga Kaduna.
Kwamishinan ’Yan Sandan Abuja, Olatunji Rilwan Disu, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce jami’an rundunar yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin Mustapha Muhammed, sun tare hanyar ’yan bindigar, inda suka yi musayar wuta da su.
“Mun yi nasarar kawar da barazana babba da ke addabar al’umma da hanyoyi,” in ji Disu.
An gano cewa Mohammed, mai shekaru 21, yana ɗaya daga cikin manyan ’yan bindigar da ke aiki a dajin Rijana na Kaduna.
“Ya sace mutane da yawa, ciki har da kashe jami’an tsaro da fararen hula.
“Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar AK-49, harsasai 60, da kuma Naira miliyan uku, da ake zargin kuɗin fansa ne da suka samu daga garkuwa da mutane,” in ji shi.
Bincike ya tabbatar da cewa ɗan bindigar na da hannu a kai hare-hare kauyukan Kike da Bagada, inda ya jagoranci garkuwa da mutane tare da karɓar kuɗin fansa.
“Ayyukansa sun jefa jama’a cikin fargaba, amma jami’anmu sun aika da saƙo mai ƙarfi cewa ba za a lamunci aikata laifi ba,” in ji Disu.
Wani jami’in ’yan sanda ya samu rauni kaɗan a yayin artabun, amma an ba shi kulawar da ya dace, inda yake murmurewa.
A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da farautar sauran ‘yan bindigar da suka tsere tare da rushe duk wani sansanin ’yan bindiga da ke iyakar Abuja da Kaduna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Ƙasurgumin Ɗan Bindiga musayar wuta yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙungiyyar Ƙwallon yashi ta Kada BSC ta fatattaki Kebbi BSC
A wasan farko na gasar cin kofin ƙwallon yashi wato Beach Soccer da aka fara gudanarwa yau Alhamis a babban birnin tarayya Abuja, Kada BSC ta lallasa Kebbi BSC da ci 8 – 5.
Kada ta samu nasarar zura ƙwallayen ne ta hannun Frank Dozievda da ya zura 4 a raga, sai Sani Hassan 2, sai kuma Hammed Kareem shi ma da ya zura ƙwallaye 2 a raga.
Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a NajeriyaA ɓangaren Kebbi United kuwa ‘yan wasan na biyar ne kowanne ya zura ƙwallo a raga da suka haɗa da: Isyaku Atiku da Ibrahim Malami da Sadik Umar da Abdullahi Aliyu da Usman Bello.
An karrama ɗan wasa Frank Dozie na Kada BSC saboda bajintar da ya nuna a wasan.
Wasa na gaba da misalin ƙarfe 4:15 na yamma
Kebbi United BSC zata kece raini da Jigawa Golden Stars BSC sai kuma ƙarfe 5:15 inda Kebbi Fishers zata fafata da Anambra Warriors a filin wasa na Jabi Lake Park da ke Abuja.