’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja
Published: 13th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga, Salisu Mohammed, wanda aka fi sani da Dogo Saleh, a wani artabu da suka yi da shi a dajin Gidan-Abe da ke kan iyakar Bwari da Kaduna.
Sun samu nasarar ne bayan samun bayanan sirri kan shigowar ‘yan bindiga yankin daga Kaduna.
Kwamishinan ’Yan Sandan Abuja, Olatunji Rilwan Disu, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce jami’an rundunar yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin Mustapha Muhammed, sun tare hanyar ’yan bindigar, inda suka yi musayar wuta da su.
“Mun yi nasarar kawar da barazana babba da ke addabar al’umma da hanyoyi,” in ji Disu.
An gano cewa Mohammed, mai shekaru 21, yana ɗaya daga cikin manyan ’yan bindigar da ke aiki a dajin Rijana na Kaduna.
“Ya sace mutane da yawa, ciki har da kashe jami’an tsaro da fararen hula.
“Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar AK-49, harsasai 60, da kuma Naira miliyan uku, da ake zargin kuɗin fansa ne da suka samu daga garkuwa da mutane,” in ji shi.
Bincike ya tabbatar da cewa ɗan bindigar na da hannu a kai hare-hare kauyukan Kike da Bagada, inda ya jagoranci garkuwa da mutane tare da karɓar kuɗin fansa.
“Ayyukansa sun jefa jama’a cikin fargaba, amma jami’anmu sun aika da saƙo mai ƙarfi cewa ba za a lamunci aikata laifi ba,” in ji Disu.
Wani jami’in ’yan sanda ya samu rauni kaɗan a yayin artabun, amma an ba shi kulawar da ya dace, inda yake murmurewa.
A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da farautar sauran ‘yan bindigar da suka tsere tare da rushe duk wani sansanin ’yan bindiga da ke iyakar Abuja da Kaduna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Ƙasurgumin Ɗan Bindiga musayar wuta yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan ta Kudu : Ana tsare da Riek Machar a wani gida
Bayanai daga Sudan ta kudu na nuni da cewa ana tsare damataimakin shugaban kasar na farko Riek Machar a wani gida, lamarin da MDD ta nuna matukar damuwa na yiwuwar komawar kasar wani yakin basasa.
Rahotanni sun ce a yammacin jiya Laraba jami’an tsaron Sudan ta Kudu sun tsare Riek Machar, kamar yadda kakakinsa ya sanar.
Ba a fayyace ainihin dalilin wannan tsarewar da kuma tasirinta ga dorewar yarjejeniyar zaman lafiya da aka rattabawa hannu a shekarar 2018 ba.
Tun a farkon watan Maris ne dai ake ta rade-radin kame Riek Machar, lokacin da rikicin yankin Upper Nile da ke arewa maso gabashin kasar ya kai ga kame wasu jami’an jam’iyyarsa a Juba.
tsare Mista Machar madugun ‘yan adawa na kasar na jefa shakku sosai kan shirin samar da zaman lafiya a Sudan ta Kudu a cewar masana.