Aminiya:
2025-05-01@04:46:07 GMT

’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja

Published: 13th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga, Salisu Mohammed, wanda aka fi sani da Dogo Saleh, a wani artabu da suka yi da shi a dajin Gidan-Abe da ke kan iyakar Bwari da Kaduna.

Sun samu nasarar ne bayan samun bayanan sirri kan shigowar ‘yan bindiga yankin daga Kaduna.

NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

Kwamishinan ’Yan Sandan Abuja, Olatunji Rilwan Disu, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce jami’an rundunar yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin Mustapha Muhammed, sun tare hanyar ’yan bindigar, inda suka yi musayar wuta da su.

“Mun yi nasarar kawar da barazana babba da ke addabar al’umma da hanyoyi,” in ji Disu.

An gano cewa Mohammed, mai shekaru 21, yana ɗaya daga cikin manyan ’yan bindigar da ke aiki a dajin Rijana na Kaduna.

“Ya sace mutane da yawa, ciki har da kashe jami’an tsaro da fararen hula.

“Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar AK-49, harsasai 60, da kuma Naira miliyan uku, da ake zargin kuɗin fansa ne da suka samu daga garkuwa da mutane,” in ji shi.

Bincike ya tabbatar da cewa ɗan bindigar na da hannu a kai hare-hare kauyukan Kike da Bagada, inda ya jagoranci garkuwa da mutane tare da karɓar kuɗin fansa.

“Ayyukansa sun jefa jama’a cikin fargaba, amma jami’anmu sun aika da saƙo mai ƙarfi cewa ba za a lamunci aikata laifi ba,” in ji Disu.

Wani jami’in ’yan sanda ya samu rauni kaɗan a yayin artabun, amma an ba shi kulawar da ya dace, inda yake murmurewa.

A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da farautar sauran ‘yan bindigar da suka tsere tare da rushe duk wani sansanin ’yan bindiga da ke iyakar Abuja da Kaduna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari Ƙasurgumin Ɗan Bindiga musayar wuta yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar yankin Borno ta Kudu, ya bayyana cewa hare-haren na ƙara ƙamari a yankin abun takaici ne.

Ya ce ya samu rahoto tsakanin Hawul da Garkida inda aka ce an kashe ’yan sa-kai sama da 10 a ranar Litinin.

A cewarsa, sama da mutane 100 aka kashe cikin wata guda a hare-hare da aka kai Sabon Gari, Izge, Kirawa, Pulka, Damboa, Chibok, Askira Uba da wasu garuruwa da dama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar