Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPC ya ce yarjejeniyar da ya ƙulla da Matatar Dangote domin sayar mata da ɗanyen man fetur a farashin naira za ta ƙare a wannan wata na Maris.

Sai dai kamfanin ce yana tattaunawa da Matatar Dangote domin tsawaita yarjejeniyar sayar mata da ɗanyen mai a naira.

An hana tashe bana a Kano — Nalako NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya

Sanarwar ta NNPC na zuwa ne bayan wasu rahotonni sun ce kamfanin ya dakatar da sayar wa matatar mai a farashin naira, kamar yadda suka ƙulla yarjejeniya tun da farko.

Wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin Olufemi Soneye ya fitar a ranar Litinin ta ce ba haka lamarin yake, yana mai cewa sai a ƙarshen watan nan na Maris yarjejeniyar za ta ƙare.

“Ya kamata a fahimci cewa yarjejeniyar sayar da ɗanyen mai a farashin naira ta wata shida ce, kuma da sharaɗin akwai man, wadda za ta ƙare a ƙarshen watan Maris na 2025.

“A ƙarƙashin wannan yarjejeniyar mun sayar wa Matatar Dangote gangan miliyan 48 ta ɗanyen man fetur tun daga watan Oktoba na 2024 zuwa yanzu.

“A yanzu muna ci gaba da tattaunawa domin ƙulla wata sabuwar yarjejeniya,” in ji shi.

Masana na cewa idan NNPC ya daina sayar wa Matatar Dangote mai a naira hakan zai iya haddasa hauhawar farashin man, maimakon sauƙin da ake tunanin hakan ya jawo a baya-bayan nan.

Dangote da NNPC sun rage farashi a gidajen mai

A makon jiya ne NNPC ya rage farashin litar man fetur a gidajen mansa da ke faɗin Nijeriya kwanaki bayan matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin man a gidajen sayar da mai masu alaƙa da ita.

Ɗaya daga cikin manyan dillalan man fetur a Najeriya ya tabbatar da cewa a yanzu “NNPC na sayar muna da man fetur ne kan naira 840 a Legas, sai kuma naira 875 a Calabar da kuma Fatakwal.”

Hakan na zuwa ne kimanin mako ɗaya bayan Matatar Dangote ta sanar da rage farashin litar man, inda mutanen Nijeriya ke sayen fetur ɗin cikin farashin da ya yi ƙasa da na NNPC a gidajen man da ke haɗin gwiwa da matatar.

Wannan ya sanya aka riƙa ganin dogayen layukan ababen hawa a gidajen man fetur ɗin da ke da alaƙa da matatar ta Dangote.

Farashin da Dangote ya sanar zai riƙa sayar wa dillalai abokan hulɗarsa shi ne naira 825 daga 890, ragin naira 65 ke nan kan kowace lita.

Karo na biyu ke nan kamfanin yana rage farashin man a watan Fabrairun 2025, abin da dillalan man suka bayyana da “abin a yaba.”

Rage farashin ya sa man na Dangote ya zama mafi rahusa idan aka kwatanta da wanda ake shigo da shi ƙasar daga ƙetare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗanyen Man Fetur Matatar Dangote sayar wa Matatar a farashin naira sayar wa matatar Matatar Dangote rage farashin za ta ƙare

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin

Gwamnatin Iraki ta bayyana cewa: Yarjejeniyar da Iran ta kulla da Iraki zata yi gagarumar amfani a fagen tsaron yankin

Ofishin jakadancin Iraki a Amurka ya tabbatar da cewa: Iraki kasa ce mai cin gashin kanta kuma tana da hakkin kulla yarjejeniyoyin da kuma yarjejeniyar fahimtar juna. An yi nuni da cewa, yarjejeniyar tsaro da aka rattabawa hannu a baya-bayan nan tsakanin Iran da Iraki ta zo ne a cikin tsarin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu don tabbatar da tsaro da kuma kula da kan iyakokin kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa: Ofishin jakadancin ya bayyana a cikin wata sanarwa da kamfanin dillancin labaran kasar Iraki INA ya watsa cewa: “A matsayin martani ga kalaman da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta yi a yayin taronta na ‘yan jarida na baya-bayan nan, Iraki kasa ce mai cikakken ‘yancin kai, kuma tana da hakkin kulla yarjejeniyoyin da kuma bayanan fahimtar juna bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulkinta da dokokin kasa, kuma ta hanyar da ta dace da manyan muradunta.”

Ta kara da cewa, “Iraki na jin dadin huldar sada zumunci da hadin gwiwa da kasashe da dama a duniya, ciki har da kasashe makwabta, Amurka, da sauran kasashe abokantaka, kuma tana da sha’awar gina wannan dangantakar bisa tushen mutunta juna da moriyar juna.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida  August 13, 2025 Wakilan Hamas sun isa Alkahira don shawarwarin tsagaita wuta a Gaza August 13, 2025 Iran: Amurka Da Isra’ila Ne Da Kansu Suka Bukaci Dakatar Da Bude Wuta August 13, 2025 Habasha: Madatsar ruwanmu amfanin dukkanin kasashen yankin ne August 13, 2025 Bankin Duniya Zai Kashe $300m Don Inganta Rayuwar ’Yan Gudun Hijira A Arewacin Nijeriya August 13, 2025 Nijeriya Da Isra’ila Na Kara Karfafa Alaka A Tsakaninsu August 13, 2025 Kasashe 27 Sun Bukaci Isara’ila Ta Kawo Karshen Hana Shigar Da Abinci A Gaza August 12, 2025 Iran: Duk Wani Sabon Hari, Zai Fuskanci Mummunan Martanin Soji August 12, 2025 Larijani: Iraki Ba Ta Karbar Umarni Daga Iran August 12, 2025 Iran: Ma’aikatar Harkokin Waje Ce Ke Kula Da Lamarin Makamashin Nukliyar Kasar August 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Wani Mummunan Hari Kan Gaza Tare Da Rusa Gidajen Mutane A Khan Yunis
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Ƙudiri – Kamfani.
  • Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
  • ‘Zan iya shiga mummunan yanayi idan Dangote bai aure ni ba’
  • Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita