Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPC ya ce yarjejeniyar da ya ƙulla da Matatar Dangote domin sayar mata da ɗanyen man fetur a farashin naira za ta ƙare a wannan wata na Maris.

Sai dai kamfanin ce yana tattaunawa da Matatar Dangote domin tsawaita yarjejeniyar sayar mata da ɗanyen mai a naira.

An hana tashe bana a Kano — Nalako NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya

Sanarwar ta NNPC na zuwa ne bayan wasu rahotonni sun ce kamfanin ya dakatar da sayar wa matatar mai a farashin naira, kamar yadda suka ƙulla yarjejeniya tun da farko.

Wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin Olufemi Soneye ya fitar a ranar Litinin ta ce ba haka lamarin yake, yana mai cewa sai a ƙarshen watan nan na Maris yarjejeniyar za ta ƙare.

“Ya kamata a fahimci cewa yarjejeniyar sayar da ɗanyen mai a farashin naira ta wata shida ce, kuma da sharaɗin akwai man, wadda za ta ƙare a ƙarshen watan Maris na 2025.

“A ƙarƙashin wannan yarjejeniyar mun sayar wa Matatar Dangote gangan miliyan 48 ta ɗanyen man fetur tun daga watan Oktoba na 2024 zuwa yanzu.

“A yanzu muna ci gaba da tattaunawa domin ƙulla wata sabuwar yarjejeniya,” in ji shi.

Masana na cewa idan NNPC ya daina sayar wa Matatar Dangote mai a naira hakan zai iya haddasa hauhawar farashin man, maimakon sauƙin da ake tunanin hakan ya jawo a baya-bayan nan.

Dangote da NNPC sun rage farashi a gidajen mai

A makon jiya ne NNPC ya rage farashin litar man fetur a gidajen mansa da ke faɗin Nijeriya kwanaki bayan matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin man a gidajen sayar da mai masu alaƙa da ita.

Ɗaya daga cikin manyan dillalan man fetur a Najeriya ya tabbatar da cewa a yanzu “NNPC na sayar muna da man fetur ne kan naira 840 a Legas, sai kuma naira 875 a Calabar da kuma Fatakwal.”

Hakan na zuwa ne kimanin mako ɗaya bayan Matatar Dangote ta sanar da rage farashin litar man, inda mutanen Nijeriya ke sayen fetur ɗin cikin farashin da ya yi ƙasa da na NNPC a gidajen man da ke haɗin gwiwa da matatar.

Wannan ya sanya aka riƙa ganin dogayen layukan ababen hawa a gidajen man fetur ɗin da ke da alaƙa da matatar ta Dangote.

Farashin da Dangote ya sanar zai riƙa sayar wa dillalai abokan hulɗarsa shi ne naira 825 daga 890, ragin naira 65 ke nan kan kowace lita.

Karo na biyu ke nan kamfanin yana rage farashin man a watan Fabrairun 2025, abin da dillalan man suka bayyana da “abin a yaba.”

Rage farashin ya sa man na Dangote ya zama mafi rahusa idan aka kwatanta da wanda ake shigo da shi ƙasar daga ƙetare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗanyen Man Fetur Matatar Dangote sayar wa Matatar a farashin naira sayar wa matatar Matatar Dangote rage farashin za ta ƙare

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda

Kotun Kolin Najeriya ta soke afuwar da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya yi wa Maryam Sanda, inda ta ce shugaban ya wuce makadi da rawa ta hanyar yin afuwa ga wacce har yanzu kararta ke gaban kotu.

A hukuncin da aka yanke ranar Juma’a, kotun ta yanke hukunci da rinjayen alƙalai huɗu cikin biyar, inda ta tabbatar da hukuncin kisa da Babban Kotun Abuja ta yanke, kuma Kotun Daukaka Kara ta tabbatar.

‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’ Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa

An yanke wa Sanda hukunci ne a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, a lokacin rikicin cikin gida a gidansu da ke Abuja.

Kotun ta yi watsi da ƙarar da ta shigar, tana mai cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da laifin kisan kai ba tare da wata shakka ba.

A hukuncin jagoran alkalan, Mai Shari’a Moore Adumein ya ce Kotun Daukaka Kara ta yi daidai wajen tabbatar da hukuncin kotun farko.

Ya ce shiga tsakani na shugaban ƙasa bai dace ba a irin wannan yanayi.

Mai Shari’a Adumein ya ce: “Ba daidai ba ne ga bangaren zartarwa ya yi ƙoƙarin amfani da ikon afuwa kan laifin kisan kai, wanda har yanzu kararsa na gaban kotu.”

A watan Oktoba, an rage hukuncin Maryam zuwa shekaru 12 a kurkuku bayan Shugaba Tinubu ya amince da jerin sunayen wadanda ya yi wa afuwa.

Wannan mataki ya biyo bayan nazari da ya fara da sunaye 175, kafin daga baya a cire wasu saboda irin laifukan da suka aikata.

A lokacin, Mai Ba da Shawara na Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce rage hukuncin Sanda “ya dogara ne da tausayi saboda amfanin ’ya’yanta da kuma kyakkyawan halinta,” sannan ya ce ta nuna “nadama.”

Wannan mataki ya janyo suka a fadin Najeriya, ciki har da adawa daga dangin marigayi Bello.

Hukuncin na Kotun Kolin yanzu dai ya soke afuwar ta Shugaban Ƙasa.

Maryam Sanda ta shafe kusan shekaru shida a kurkuku, kuma hukuncin da aka rage zai bar ta da kusan shekaru shida nan gaba. Amma da hukuncin na ranar Juma’a, an dawo da hukuncin kisa da aka yanke mata tun farko.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon  A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699
  • Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta