Gina Mutane Don Bunkasa Hazakarsu Na Daga Cikin Ajendar Sin Na 2025
Published: 10th, March 2025 GMT
Kirkira ita ce kashin bayan ci gaba, kuma hazaka ita ce ginshikin kirkira. A zamanin yau, fannoni masu tasowa musamman na fasahar zamani kamar kirkirarriyar basira (AI) da sauransu suna bunkasa, kuma akwai bukatu na matukar gaggawa ga sabbin hazaka. Hakan ya sanya kasar Sin ta maida hankali kan raya hazaka tun wuri-wuri, da kara zuba jari a fannin ilimi, da dasa iri na kirkire-kirkire don ya tsira a cikin zukatan matasa ta hanyar “zuba jari kan gina mutane”.
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron tattaunawa da nazari kan ganawar da wakilan jam’iyyar CPPCC daga fannonin kimiyya, fasaha da ilimi, wanda ya fitar da kwakkwaran matakai game da hangen nesa a ranar 6 ga watan nan da muke ciki, wanda ya jaddada muhimmancin kimiyya da fasaha da ilimi da hazaka ga zamanantar da kasar Sin, inda shugaba Xi ya jaddada cewa a nan gaba, ya kamata kasar Sin ta rungumi wani yanayi mai haske, inda za a samu masu kwazo da hazaka masu dimbin yawa, ta yadda kowa da kowa zai baje kolin basirarsa kuma a yi amfani da su yadda ya kamata. Har ila yau, a cikin rahoton aikin gwamnati na bana, an gabatar da sabbin dabarun “zuba jari kan gina mutane” a karon farko, wanda kamar fitila, ya haskaka muhimmin alkibla ga ci gaban kasar Sin a nan gaba. Sanin kowa ne cewa, a cikin ’yan shekarun nan, gwamnatin kasar Sin a dukkan matakai ta samu sakamako mai ban mamaki a fannonin zuba jari na zahiri wadanda suka shafi ababen more rayuwa, da kawo sabbin salon gudanar da harkokin birane da kauyuka. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
Wasu abubuwan fashewa da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram ne suka dasa, sun kashe kimanin mutane 26, ciki har da mata da ƙananan yara a kusa da garin Rann da ke Ƙaramar Hukumar Kala Balge ta Jihar Borno.
Majiyoyin tsaro da na cikin gari sun bayyana cewa mutane da dama sun jikkata bayan da motar da ke ɗauke da wadanda abin ya shafa zuwa Gambarou Ngala ta taka abin fashewar.
Wata majiya ta ce, “Ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma rahotanni na farko sun nuna cewa mata huɗu da yara shida da maza 16 ne suka mutu a wannan fashewar.”
Ta ci gaba da cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Furunduma, kimanin kilomita 11 daga garin Rann, da misalin karfe 11 na safe a ranar Litinin.
Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin NajeriyaTa ƙara da cewa an kai wasu da suka jikkata asibitin Rann domin kula da su.
Babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren sojoji ko ’yan sanda game da faruwar lamarin.
Sai dai kuma, kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, Kenneth Daso, bai yiwu ba saboda layin wayarsa ba ya shiga.