Leadership News Hausa:
2025-10-18@23:18:00 GMT

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

Published: 10th, March 2025 GMT

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

Wasu ‘yan bindiga sun farmaki gidan Alhaji Yusha’u Ma’aruf, mamallakin wani asibiti mai zaman kansa, a garin Zakirai da ke ƙaramar hukumar Gabasawa a jihar Kano, inda suka sace wani matashi mai shekaru 20 tare da jikkata ɗan uwansa.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan uku ɗauke da bindigogi da adduna sun afka wa gidan da misalin ƙarfe 2:15 na dare, suka sare yatsan hannun Abubakar Yusha’u mai shekaru 23 sannan suka sace ɗan uwansa, Mohammed Bello Yusha’u.

Daily Trust ta ruwaito cewa, sun kwashe wayoyi da kuɗaɗe kafin su tsere.

Tinubu Ya Buƙaci A Mayar Wa BUK Filin Rimin Zakara Da Ake Taƙaddama A Kai Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC

Kakakin rundunar ‘yansandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa jami’an tsaro sun fara bincike don ceto wanda aka sace da kuma kamo waɗanda suka aikata harin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zikirai

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu na ƙoƙarin mayar da Najeriya mai jam’iyya ɗaya — ADC

Jam’iyyar ADC ta ce sauya sheƙar da wasu gwamnonin jihohi suka yi zuwa jam’iyya mai mulki ya nuna yadda Shugaba Bola Tinubu, ke ƙoƙarin mayar da Najeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya.

A wata sanarwa da Bolaji Abdullahi, mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, ya fitar, ya ce jam’iyyun adawa ba su damu da abin da ya kira “cin amanar siyasa” da gwamnonin suka yi ba.

Gwamna Inuwa ya naɗa sabbin shugabanni a ma’aikatar lafiya ta Gombe Ba za mu yi sulhu da ’yan bindiga ba sai sun yi tuba na gaskiya — Radda

Ya ce zaɓen 2027 ba zai zama takara tsakanin jam’iyyu kawai ba, sai dai ya zama gwagwarmaya tsakanin talakawan Najeriya da gwamnatin da ta jefa rayuwar talakawa cikin wahala.

Abdullahi, ya bayyana cewa komawar gwamnonin jihohin Enugu da Bayelsa zuwa jam’iyyar APC, ta tabbatar da cewa Shugaba Tinubu, na da niyyar raunana dimokuraɗiyya da jam’iyyun adawa a ƙasar nan.

Ya ƙara da cewa duk da cewar gwamnonin sun koma jam’iyya mai mulki a zahirin gaskiya sun bar jama’arsu ne tare da komawa jam’iyyar da ta gaza ciyar da ƙasa gaba.

A cewar Abdullahi, ’yan Najeriya da dama suna cikin wahala saboda gazawar gwamnatin APC, hauhawar farashin kayan abinci, rashin ayyukan yi, matsalar tsaro, rashin ingantaccen tsarin kiwon lafiya, da cin hanci da rashawa.

Ya ce ’yan Najeriya sun yi tsammanin gwamnonin adawa za su yi tsayin daka su kare jama’a da kawo mafita, amma maimakon haka, wasu daga cikinsu sun shiga jam’iyyar mai mulki saboda son rai.

Abdullahi, ya kuma ce duk da APC na murna da samun waɗancan gwamnoni, ADC da sauran jam’iyyun adawa suna farin ciki saboda yanzu ’yan Najeriya za su iya gane waɗanda za su tsaya domin ceto ƙasar nan.

Ya ƙarƙare da cewa zaɓen 2027 zai zama takara kai-tsaye tsakanin talakawan Najeriya da gwamnatin Shugaba Tinubu ta jam’iyyar APC.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano
  • HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya
  • Gaza Ta Bukaci A Binciki Isra’ila Kan Sace Sassan Jiki A Gawarwakin Falasdinawa
  • Gaza ta bukaci a binciki Isra’ila kan sace sassan jiki a gawarwakin falasdinawa
  • Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
  • Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo
  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe
  • An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.
  • Tinubu na ƙoƙarin mayar da Najeriya mai jam’iyya ɗaya — ADC