Aminiya:
2025-11-18@10:41:34 GMT

Tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa na fuskantar zargin zamba

Published: 9th, March 2025 GMT

Wata kotu a Birnin Paris na Ƙasar Faransa, ta samu tsohon shugaban hukumar tsaron cikin gida ta Faransa, Bernard Squarcini, da laifin zamba da amfani da dukiyar jama’a ba bisa ƙa’ida ba.

Squarcini, mai shekaru 69, ya jagoranci hukumar tsaron cikin gida ta Faransa daga 2008 zuwa 2012.

Makahon da ke sana’ar POS Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto

Bayan ya bar aiki, kamfanin LVMH ya ɗauke shi aiki a matsayin mai bayar da shawara kan harkokin tsaro.

A ranar Juma’a da ta gabata, kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru huɗu a gidan yari, inda biyu daga ciki aka dakatar da su.

An same shi da laifin amfani da abokan tsaronsa don cimma burinsa, har da samun bayanan sirri na kamfanin LVMH.

Za a ba Squarcini damar yin zaman gidansa, amma sanye da munduwa ta lantarki.

Haka kuma, an ci shi tarar Yuro 200,000 tare da dakatar da shi daga duk wani aiki da ya shafi leƙen asiri ko bayar da shawara na tsawon shekaru biyar.

Lauyoyinsa sun ce za su ɗaukaka kara kan hukuncin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faransa Tsohon Shugaban Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Kamar ‘yan wasa da masu horarwa, an hana jami’an wasa shiga ayyukan yin caca bisa ga ka’idojin TFF, da kuma na FIFA da hukumar gudanarwa ta Turai (Uefa), masu gabatar da kara na Turkiyya sun bayar da umarnin tsare mutane 21 ciki har da alkalai 17 da shugabannin kungiyoyin kwallon kafa biyu a wani bangare na babban bincike kan yin caca da kuma shirya yadda sakamakon wasa zai iya fitowa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi November 15, 2025 Wasanni Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika November 15, 2025 Wasanni Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe November 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu shigar da kara na ICC sun bukaci hukuncin daurin rai da rai a kan kwamandan RSF
  • Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan
  • ’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC
  • An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
  • Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato
  • Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasa
  • Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca