Aminiya:
2025-07-03@03:28:16 GMT

Tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa na fuskantar zargin zamba

Published: 9th, March 2025 GMT

Wata kotu a Birnin Paris na Ƙasar Faransa, ta samu tsohon shugaban hukumar tsaron cikin gida ta Faransa, Bernard Squarcini, da laifin zamba da amfani da dukiyar jama’a ba bisa ƙa’ida ba.

Squarcini, mai shekaru 69, ya jagoranci hukumar tsaron cikin gida ta Faransa daga 2008 zuwa 2012.

Makahon da ke sana’ar POS Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto

Bayan ya bar aiki, kamfanin LVMH ya ɗauke shi aiki a matsayin mai bayar da shawara kan harkokin tsaro.

A ranar Juma’a da ta gabata, kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru huɗu a gidan yari, inda biyu daga ciki aka dakatar da su.

An same shi da laifin amfani da abokan tsaronsa don cimma burinsa, har da samun bayanan sirri na kamfanin LVMH.

Za a ba Squarcini damar yin zaman gidansa, amma sanye da munduwa ta lantarki.

Haka kuma, an ci shi tarar Yuro 200,000 tare da dakatar da shi daga duk wani aiki da ya shafi leƙen asiri ko bayar da shawara na tsawon shekaru biyar.

Lauyoyinsa sun ce za su ɗaukaka kara kan hukuncin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faransa Tsohon Shugaban Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba

Majalisar Dokokin Jihar Filato ta zaɓi Nanloong Daniel a matsayin sabon Kakakin Majalisar, bayan da Gabriel Dewan ya yi murabus.

Zaɓen sabon kakakin ya gudana ne a wani zaman gaggawa da majalisar ta gudanar ranar Laraba.

David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana

Zaman ya gudana ne a harabar tsohon gidan gwamnatin jihar.

Hon. Nanloong Daniel, wanda ke wakiltar mazaɓar Mikang wanda kuma tsohon jagoran masu rinjaye ne a majalisar ta tara, ya samu amincewar dukkanin ’yan majalisar 24 don jagorantar su.

Daniel shi ɗan jam’iyyar APC ne.

Zaɓen nasa ya biyo bayan wani zaman sirri da aka yi tsakanin Gwamna Caleb Mutfwang, tsohon kakakin majalisar Dewan, da sauran ’yan majalisar, domin warware rikicin shugabanci da ke damun majalisar.

Mataimakin akakin ajalisar, Hon. Gwotta Ajang, ne ya jagoranci zaman gaggawar tare da kula da sauyin shugabancin cikin lumana.

Dewan, wanda shi kaɗai ne ɗan jam’iyyar YPP, daga yankin Filato ta Tsakiya, ya ajiye muƙaminsa domin taimakawa wajen kawo ƙarshen rikicin siyasar jihar.

Murabus ɗinsa na zuwa ne bayan wani dogon lokaci aka kwashe ana rikici bayan korar wasu ’yan majalisar jam’iyyar PDP daga majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • Kotu A Kasar Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Ayatullahi Baqir Sadr
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kakkausar Suka Kan Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta IAEA
  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce; Dokar Majalisar Shawarar Musulunci Ta Kasar Kan Hukumar IAEA Dole Ne Aiki Da Ita
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe