A ko da yaushe kasar Sin na tsayawa tare da kasashe masu tasowa a matsayinta na kasa mai tasowa kuma mamba na wadannan kasashe.

Kakakin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, Lou Qinjian ne ya bayyana hakan a ranar Talata a taron manema labarai, inda ya ce, kasar Sin za ta rika shiga a dama da ita, kuma za ta kasance mai bayar da shawarwari kan hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa.

Da yake tsokaci game da matakin da Amurka ta dauka na sanya karin harajin kashi 10 cikin 100 kan kayayyakin da ake shigar da su daga kasar Sin, Lou ya ce, daukar matakin da Amurka ta yi bisa radin kai ya saba wa ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya, kuma ya kawo cikas ga tsaro da zaman lafiyar masana’antu da tsarin samar da kayayyaki a duniya. Kakakin ya kara da cewa, kamata ya yi Amurka ta yi aiki tare da kasar Sin kuma su fahimci juna don warware takaddamar cinikayya ta hanyar yin shawarwari bisa daidaici.

Ya kuma kara da cewa, kasar Sin tana matukar martaba dangantakarta da kasashen Turai, kuma sassan biyu abokan hulda ne dake ba da gudummawa ga samun nasarar juna. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya soki lamirin kasar Amurka, dangane da yadda ta wanke Japan daga laifukan da ta tafka, yayin yakin duniya na biyu. Jiang Bin, wanda ya yi sukan a Juma’ar nan, ya kira hakan a matsayin mummunan karan-tsaye ga ainihin abun da ya auku a tarihi, kana tozarta damuwar wadanda mamayar dakarun Japan ta cutar.

Jami’in ya yi tsokacin ne a matsayin martani ga sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar, inda ta ce, bana shekaru 80 ke nan, bayan da Amurka da Japan suka kawo karshen yaki a yankin tekun Pacific. To sai dai kuma a ta bakin Jiang Bin, yayin yakin duniya na biyu, dakarun Japan ‘yan mamaya sun aikata muggan laifuka, tare da muzgunawa al’ummun sassan duniya daban daban, ciki har da na Amurka. Amma abun mamaki sai ga shi a yanzu bangaren Amurka ya manta da hakan.

Don haka dai Sin na kira ga Amurka da ta yi watsi da dabarun siyasar yankuna, ta martaba abubuwan da suka wakana a tarihi yayin yakin duniya na biyu, kana ta hada hannu da sassan kasa da kasa, wajen kare tsarin cudanyar sassan duniya bayan shudewar yakin duniya na biyu. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • India Ta Dage Kan Maida martani da hana Shigowar Kayakin Amurka Kasar
  • Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Gwamnatin Mali Ta Bankado Wata Makarkashiyar Janyo Hargitsi A Kasar Tare Da Wargaza Shi
  • Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
  • Iran Ta Bukaci Mayar Da Martani Kan Aniyar Isra’ila Ta Mamaye Yankunan Kasashe Domin Kafa ‘Babbar Isra’ila’
  • Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
  • Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: A Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Jaddada Kasancewar Iran Tare Da Kasar Lebanon Koda Yaushe