Pezeshkian: Wajibi Ne Kasashen Musulmi Su Kara Karfafa Alakokinsu
Published: 28th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce inganta hadin kai da alaka tsakanin kasashen musulmi da suka hada da Iran da Malaysia na daga cikin abubuwan da ake bukata a halin da ake ciki a duniya.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ta yi da ministan harkokin wajen Malaysia Dato’ Seri Utama Haji Mohamad Bin Haji Hasan a birnin Tehran a wata ziyara da ya kai kasar Iran.
Ya ce a halin yanzu gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana aiwatar da abin da take yin a laifuka da wuce gona da iri a yankin saboda kan musuylmi ba hade yake ba.
Ya kara da cewa samar da hadin kai tsakanin jami’ai da ‘yan siyasar kasashen musulmi zai taka muhimmiyar rawa wajen kawar da bambance-bambance, rashin fahimta da talauci a cikin kasashen musulmi.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take domin kara fadada hanyoyin sadarwa da kasashen musulmi ciki har da Malaysia a dukkan fannoni in ji shugaban na Iran.
A ci gaba da jawabin nasa, Pezeshkian ya yi nuni da cewa, an gudanar da taron kwamitin hadin gwiwa na kasashen Iran da Malaysia karo na 8 a birnin Tehran a safiyar Laraba bayan shafe shekaru 17 ana yin irin wannan taro.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Malaysia ya ce alakar da ke tsakanin Tehran da Kuala Lumpur ta ginu ne bisa fahimta da ‘yan uwantaka.
Ya bayyana aniyar Malaysia na bunkasa alaka da Iran da kuma amfana da karfin Jamhuriyar Musulunci ta fuskar kimiyya, fasaha, ilimi, kayan abinci da noma.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Har ila yau, Lin ya ce matsayin kasar Sin dangane da rikicin kasar Ukraine bai sauya ba, cewa tattaunawa, da gudanar da shawarwari ne kadai hanyoyi mafiya dacewa na warware rikicin. Har kullum Sin na kan turbar adalci game da rikicin, tana kuma ci gaba da ingiza bukatar komawa teburin shawara tun barkewar rikicin. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp