Pezeshkian: Wajibi Ne Kasashen Musulmi Su Kara Karfafa Alakokinsu
Published: 28th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce inganta hadin kai da alaka tsakanin kasashen musulmi da suka hada da Iran da Malaysia na daga cikin abubuwan da ake bukata a halin da ake ciki a duniya.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ta yi da ministan harkokin wajen Malaysia Dato’ Seri Utama Haji Mohamad Bin Haji Hasan a birnin Tehran a wata ziyara da ya kai kasar Iran.
Ya ce a halin yanzu gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana aiwatar da abin da take yin a laifuka da wuce gona da iri a yankin saboda kan musuylmi ba hade yake ba.
Ya kara da cewa samar da hadin kai tsakanin jami’ai da ‘yan siyasar kasashen musulmi zai taka muhimmiyar rawa wajen kawar da bambance-bambance, rashin fahimta da talauci a cikin kasashen musulmi.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take domin kara fadada hanyoyin sadarwa da kasashen musulmi ciki har da Malaysia a dukkan fannoni in ji shugaban na Iran.
A ci gaba da jawabin nasa, Pezeshkian ya yi nuni da cewa, an gudanar da taron kwamitin hadin gwiwa na kasashen Iran da Malaysia karo na 8 a birnin Tehran a safiyar Laraba bayan shafe shekaru 17 ana yin irin wannan taro.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Malaysia ya ce alakar da ke tsakanin Tehran da Kuala Lumpur ta ginu ne bisa fahimta da ‘yan uwantaka.
Ya bayyana aniyar Malaysia na bunkasa alaka da Iran da kuma amfana da karfin Jamhuriyar Musulunci ta fuskar kimiyya, fasaha, ilimi, kayan abinci da noma.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi kakkausar suka ga sabbin takunkuman da Amurka ta kakabawa kasarta
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i, ya yi kakkausar suka kan matakin da Amurka ta dauka na kakabawa wasu gungun mutane, hukumomin shari’a da jiragen ruwa masu alaka da makamashi da man fetur na Iran sabbin takunkumi.
Baqa’i ya gwada rashin amincewar Iran da bakar siyasar Amurka da na ‘yan sahayoniyya musamman farmakin da Amurka da gwamnatin sahayoniyya suka kaddamar na baya-bayan nan kan kasar Iran, yana mai bayyana kakaba takunkumin a matsayin baya da wani harumi na doka kawai matakin zalunci ne kan Iran lamarin da ke fayyace kiyayyar Amurka karara kan Iran.
Baqa’i ya kara da cewa: Al’ummar Iran suna sane da mummunar manufar wadannan tsauraran takunkumin da suke da nufin raunana Iran da neman take mata kowane irin hakki, za su tsaya da dukkan karfinsu wajen kalubalantarsu domin kare mutunci da muradunsu.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada cewa: Dabi’ar da Amurka take gudanarwa na nuna son kai da kuma bin hanyar da ba ta dace ba da tilastawa wajen cimma haramtattun manufofinta a matakin kasa da kasa, da kuma rashin mutunta tsarin doka da ‘yancin bil Adama, sun yi hannun riga da tushen dokokin kasa da kasa, gami da ka’idar mutunta ‘yancin kasashe da ‘yancin cinikayya tsakanin kasashe, da kuma daukan matakan nuna barazana ga duniya da ba a taba gani ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci