HausaTv:
2025-05-31@07:51:05 GMT

Iran Ta Yi Tir Da Kakkausar Murya Kan Barazanar Soji Da Isra’ila Ke Yi Mata

Published: 28th, February 2025 GMT

Iran ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan barazanar soji da Isra’ila ke yi mata, da kuma sukar da kasashen Yamma suka yi kan karfin tsaron kasar a matsayin rashin hankali da wauta.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baqaei ya bayyana a jiya Alhamis yayin da jami’an Isra’ila ke ci gaba da yi wa Iran barazanar daukar matakin soji, kasashen yamma na ci gaba da zargin kasar da kara karfin tsaronta.

M. Baqaei ya yi nuni da cewa, yankin yammacin Asiya na fama da wata mamaya da ta dade wacce kamu ta wuce gona da iri da rashin bin doka da oda.

Don haka ya kara da cewa, wajibi ne kawai Iran ta kara karfin tsaronta.

Kalaman nasa sun zo ne bayan ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce ana bukatar daukar matakin soji don dakatar da shirin nukiliyar Iran.

A cikin shekarun da suka gabata, kasashen Yamma sun soki ayyukan Iran a kan shirin nukiliyarta, jirage marasa matuka, tsaron sararin samaniyarta, da kuma shirye-shiryen makamai masu linzaminta, suna masu neman Tehran ta dakatar da su.

Iran ta sha nanata cewa ci gaban da take samu na soji ne kawai don kara kaimi ga kasar kan barazanar abokan gaba, musamman Isra’ila da Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Yayi Tir Da Jakadan Burtaniya A Amurka Dangane Da Tashe Uranim A Kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arachi ya tir da kalaman jakadan Burtaniya a Washington,  Peter Mandelson, wanda yayi kira ga Amurka kada ta taba barin Iran ta tashe makamashin Uranium a cikin kasar. Ministan ya kara da cewa Mandelson yana son ya karkatar da tattaunawan da Iran take da Amurka.

Ya kuma kara da  cewa Iran ce take sanar da kasashen turai yadda tattaunawa tsakanin Amurka da ita ke tafiya, tun Amurka ta waresu daga tattaunawar. Yace, idan har haka ne tunanin kasar Burtaniya wacce take cikin kasashen da suka sanyawa yarjeniyar JCPOA hannu, yana ganin mai yuwa Iran ta dakatar da sanar da su abubuwan da ke tafiya a tattaunawar.

Ya zuwa zagaye har 5 wadanda Amurka da Iran suka tattaunawa dangane da shirin Nukliya na Iran dai, Iran ta nuna mata cewa hanata tace uranium a cikin gida, jan layi ne wanda ba zata amince da shi ba, kuma ya sabawa yarjeniyar NPT wacce ta bawa Iran wannan damar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
  • Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran
  • Sojojin Yemen Sun Hana Jigilar Jiragen Sama A Isra’ila Tare Da Firgita ‘Yan Sahayoniyya
  • Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  •  Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”
  • Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yayi Tir Da Jakadan Burtaniya A Amurka Dangane Da Tashe Uranim A Kasar