Kasashen Habasha da Nijar sun tattauna kan inganta hadin gwiwar soji da tsaro
Published: 28th, February 2025 GMT
Ministar tsaron Habasha Aisha Mohammed ta gana da tawagar sojoji daga Nijar karkashin jagorancin ministan tsaro Salifu Modi, inda bangarorin biyu suka tattauna kan yadda za a inganta hadin gwiwar soja da tsaro.
Ministar tsaron Habasha Aisha Mohammed ta jaddada cewa; Afirka na da karfin fuskantar kalubale ba tare da tsoma bakin waje ba.
A yayin ganawarta da tawagar sojojin kasar Nijar karkashin jagorancin ministan tsaro Salifu Modi a babban birnin kasar Adis Ababa, Mohammed ta jaddada muhimmancin karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa amincewa da mutunta juna.
Ta sake jaddada aniyar Habasha na tallafawa zaman lafiyar nahiyar da kuma inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka don fuskantar barazanar tsaro tare.
A nasa bangaren, ministan tsaron Nijar ya jaddada cewa, “Habasha babbar aminiya ce wajen inganta tsaro da zaman lafiyar yankin.”
Ya kuma bayyana burin kasarsa na cin gajiyar kwarewar kasar Habasha a fannonin horas da sojoji da inganta tsaro.
Bangarorin biyu sun tattauna kan yadda za a inganta hadin gwiwar soji da tsaro, baya ga wasu batutuwa da bangarorin biyu za su ci gajiyar juna.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
Gabanin tafiyar shugaban kasar Sin Xi Jinping birnin Astana na kasar Kazakhstan, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, an kaddamar da bikin gabatar da jerin shirye-shiryen shirye-shiryen telebijin da fina-finai, na babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG na shekarar 2025 a birnin Astana.
Za a gabatar da shirye-shiryen CMG guda 12, ciki har da alakar dake tsakanin shugaba Xi Jinping da al’adun kasar Sin, da hanyar zamanintar da kasa mai salon kasar Sin na musamman da sauransu, a manyan kafofin watsa labaru na kasashen Kazakhstan, da Kyrgyzstan, da Tajikistan, da Turkmenistan, da Uzbekistan da dai sauransu.
Shugaban gidan CMG Shen Haixiong ya bayyana cewa, a ta bakin shugaba Xi Jinping, kasar Sin kyakkyawar abokiya ce ta kasashen tsakiyar Asiya, don haka ya kamata a kara yin kokari wajen raya makomar bai daya ta Sin da kasashen tsakiyar Asiya. Kuma kafar CMG ta yi hadin gwiwa tare da kafofin watsa labaru na kasashen tsakiyar Asiya, wajen gabatar da shirye-shirye, don sa kaimi ga aiwatar da ayyukan da aka cimma, a taron koli na Sin da tsakiyar Asiya na shekarar 2023, da kara gudanar da mu’amalar al’adu, da sada zumunta a tsakaninsu bisa manufofin da shugaba Xi ya gabatar. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp