Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
Published: 27th, February 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce Gwamna Umar Namadi ya amince da nadin sabbin jami’an cibiyoyi 27 da za su gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.
Babban Daraktan Hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse babban birnin jihar.
Ya ce, an zabo sabbin jami’an cibiyar ne daga dukkan kananan hukumomin jihar 27, kuma za su samu horo da jagoranci kan ayyukan da hukumar ta dora musu.
Ya kuma bayyana cewa, tuni hukumar ta gudanar ta taron bita ga dukkan jami’an shiyyar da nufin sanar da jami’an irin ci gaban da aka samu a shirye-shiryen gudanar da aikin hajji mai zuwa.
Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya bayyana jin dadinsa kan yadda ake ci gaba da gudanar da harkokin ilimantar da Alhazan game da aikin hajjin.
Ya yi bayanin cewa, an tanadar da zababbun malaman addinin Islama domin gudanar da aikin bita ga Alhazai da ke gudana a babban masallacin Dutse.
Ya ce, hukumar jin dadin Alhazai ta jihar ta bullo da sabbin dabaru na ilmantar da Alhazan na bana.
Ya shawarci maniyyata musamman wadanda wannan ne Hajjinsu na farko, da su yi amfani da wannan dama wajen inganta iliminsu na addini da sauran muhimman bayanai da za su taimaka musu wajen gudanar da aikin hajji karbabbe.
Shugaban ya ce, nan ba da jimawa ba za a rufe gudanar da taro bitar har sai bayan watan Ramadan.
Ya ce, taron bitar da hukumar ta gudanar, ya bai wa maniyyatan jihar damar samun ilimin aikin hajji da kuma sanin tsare-tsaren da hukumomin Saudiyya da hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON suka tanadar a aikin hajjin bana.
Don haka, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yaba wa mahalarta taron bitar, inda ya kara da cewa hakan karin ilimi ne da zai amfane su baki daya.
Da yake tsokaci game da rajistar da ake ci gaba da yi a jihar, shugaban hukumar ya yi kira ga maniyyatan da suka fito daga dukkan kananan hukumomi ashirin da bakwai na jihar da har yanzu ba su kammala biyan kudin ba, su yi kokarin cikawa domin hukumar NAHCON ta kara wa’adin biyan kudin zuwa mako mai zuwa.
Labbo, ya ce ranar wa’adin zai cika ne a ranar 7 ga watan Maris 2025, inda ya kara da cewa, hukumar ta biya kusan Naira biliyan 6 ga NAHCON.
Ya kuma yabawa jami’an shiyyar da suka yi rijista, tare da tattara kudaden ajiyar hajji a yankunansu.
Shugaban hukumar, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewa da sabbin jami’an cibiyar da kuma goyon baya da hadin kai da ake ba hukumar a kowane lokaci.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
Gwamnatin Jihar Kano ta gano ma’aikatanta 240 da ke ƙarɓar albashi sau biyu a duk wata, da wasu 217 da ke amfani da lambar tantance asusun banki (BVN) guda ɗaya.
Wani mai magana da yawun gwamnati, Dakta Sulaiman Wali Sani, ya gaya wa manema labarai a ranar Lahadi cewa an gano wannan badaƙalar ce a yayin da ake tantance tsarin biyan albashin gwamnati.
Dr. Sani ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin biyan ma’aikata daidai kuma akan lokaci, kuma gano waɗannan matsalolin wani ɓangare ne na gyara al’amura.
Ya ce sun duba bayanan ma’aikata ta hanyar amfani da hotunan yatsa a matakin jiha da ƙananan hukumomi.
“Tsohuwar hanyar biyan mutane tana da matsaloli. Mun gano ma’aikata 240 suna karɓar albashi sau biyu kuma mutane 217 suna amfani da BVN ɗaya, wanda zai iya nufin akwai ma’aikatan bogi ko kuma mutane suna amfani da BVN na wani,” in ji Dakta Sani.
Ya kuma ce ma’aikata 1,335 ba su zo don a tantance su ba a tsawon fiye da watanni shida, wanda ya sa suke tunanin ko waɗannan mutanen da gaske suna aiki da gwamnati.
Alhaji Umar Idi, wanda ya duba biyan kuɗin ƙananan hukumomi, ya ce sun gano sunaye 247 da babu tabbaci a kansu. Waɗannan sun haɗa da mutanen da suka yi ritaya, waɗanda suka mutu, ko kuma waɗanda aka ci gaba da biyan su ba tare da izini ba bayan lokacin barinsu aiki.
“Daga cikin waɗannan ma’aikata 247, takwas ne kawai suka zo don tabbatar da cewa har yanzu suna aiki. Za a goge sauran sunaye 239, wanda zai rage wa gwamnati asarar naira miliyan 27 a duk wata,” in ji shi, yana mai cewa za a mayar da kuɗaɗen da aka samu ga asusun gwamnati.
Dakta Sani ya ce gwamnati ba ta ƙoƙarin hukunta kowa ba, kawai dai tana gyara tsarin ne don ma’aikata na gaske da ’yan fansho su ci gaba da karɓar haƙƙoƙinsu ba tare da wata matsala ko yanka ba bisa ƙa’ida ba.
“Tun lokacin da Gwamna Abba ya fara aiki, ya tabbatar da cewa ana biyan ma’aikatan gwamnati da ’yan fansho a kan lokaci, ba tare da ɓoyayyun cire-cire da aka riƙa yi a baya ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa yanzu da suke tsaftace tsarin biyan kuɗi, ma’aikata su yi tsammanin samun biyan kuɗi mafi inganci a gaba.
Gwamnati ta ce za ta ci gaba da magana da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa an magance duk matsalolin kuma jama’a sun sake amincewa da ayyukan gwamnati.