Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
Published: 27th, February 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce Gwamna Umar Namadi ya amince da nadin sabbin jami’an cibiyoyi 27 da za su gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.
Babban Daraktan Hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse babban birnin jihar.
Ya ce, an zabo sabbin jami’an cibiyar ne daga dukkan kananan hukumomin jihar 27, kuma za su samu horo da jagoranci kan ayyukan da hukumar ta dora musu.
Ya kuma bayyana cewa, tuni hukumar ta gudanar ta taron bita ga dukkan jami’an shiyyar da nufin sanar da jami’an irin ci gaban da aka samu a shirye-shiryen gudanar da aikin hajji mai zuwa.
Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya bayyana jin dadinsa kan yadda ake ci gaba da gudanar da harkokin ilimantar da Alhazan game da aikin hajjin.
Ya yi bayanin cewa, an tanadar da zababbun malaman addinin Islama domin gudanar da aikin bita ga Alhazai da ke gudana a babban masallacin Dutse.
Ya ce, hukumar jin dadin Alhazai ta jihar ta bullo da sabbin dabaru na ilmantar da Alhazan na bana.
Ya shawarci maniyyata musamman wadanda wannan ne Hajjinsu na farko, da su yi amfani da wannan dama wajen inganta iliminsu na addini da sauran muhimman bayanai da za su taimaka musu wajen gudanar da aikin hajji karbabbe.
Shugaban ya ce, nan ba da jimawa ba za a rufe gudanar da taro bitar har sai bayan watan Ramadan.
Ya ce, taron bitar da hukumar ta gudanar, ya bai wa maniyyatan jihar damar samun ilimin aikin hajji da kuma sanin tsare-tsaren da hukumomin Saudiyya da hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON suka tanadar a aikin hajjin bana.
Don haka, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yaba wa mahalarta taron bitar, inda ya kara da cewa hakan karin ilimi ne da zai amfane su baki daya.
Da yake tsokaci game da rajistar da ake ci gaba da yi a jihar, shugaban hukumar ya yi kira ga maniyyatan da suka fito daga dukkan kananan hukumomi ashirin da bakwai na jihar da har yanzu ba su kammala biyan kudin ba, su yi kokarin cikawa domin hukumar NAHCON ta kara wa’adin biyan kudin zuwa mako mai zuwa.
Labbo, ya ce ranar wa’adin zai cika ne a ranar 7 ga watan Maris 2025, inda ya kara da cewa, hukumar ta biya kusan Naira biliyan 6 ga NAHCON.
Ya kuma yabawa jami’an shiyyar da suka yi rijista, tare da tattara kudaden ajiyar hajji a yankunansu.
Shugaban hukumar, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewa da sabbin jami’an cibiyar da kuma goyon baya da hadin kai da ake ba hukumar a kowane lokaci.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar
Jami’an tsaron kasar Iran sun murkushe ‘yan ta’adda da suka kai hari a ofishin ‘yan sanda a kudu maso gabashin kasar
Wasu ‘yan ta’adda da ake kira “Rundunar Shari’a” sun yi yunkurin kai farmaki ofishin ‘yan sanda na Saravan da ke lardin Sistan da Baluchestan na kasar Iran a wani tsararren harin wuce gona da iri kan jami’an tsaron Iran, amma jami’an tsaron da aka tura domin kalubalantansu sun yi nasarar mayar da martani mai gauni kan ‘yan ta’addan.
A cewar majiyoyin Iran, an kashe ‘yan ta’adda uku tare da kame biyu a wadannan gumurzun.
Wani dan sanda mai suna Khodadad Baqiri Saravan ya yi shahada a wani artabu da gungun ‘yan ta’adda a birnin Saravan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124 August 10, 2025 Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa August 10, 2025 Tel Aviv: Dubban yahudawa sun yi zanga-zangar adawa da yakin Gaza August 10, 2025 Welayati: Makircin Amurka da Isra’ila na kwance damarar Hizbullah ba zai yi nasara ba August 10, 2025 Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu August 10, 2025 Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar August 10, 2025 Pezeshkiyan Ya Yabawa Yan Jarida A Ayyukansu A Yakin Kwanaki 12 August 9, 2025 Yansanda A Burtaniya Ta kama Mutane Fiye Da 200 Masu Goyon Bayan Falasdinawa August 9, 2025 Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan August 9, 2025 Falasdinawa 11 Ne Suka Rasa Rayukansu Saboda Yunwa A Gaza August 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci