Leadership News Hausa:
2025-08-18@03:38:06 GMT

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Published: 18th, May 2025 GMT

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Za ki samu kaza sai ki wanke ta, sannan ki tabbatar kin tsane mata ruwa ba’a barinta da ruwa ko kadan, sai ki zuba magi da gishiri da kori da kayan yaji da tafarnuwa idan kin so za ki dakata ko ki zuba ta haka, sai ki cakuda sosai ya shisshiga cikin kazar, sannan ki kawo albasa ki zuba wanda dama kin yankata a kwance ko a tsaye ba kanana ba saboda katta narke.

Sai ki kawo jajjagen tattasanki ki zuba, sai ki sake gaurayawa sosai, sannan ki ware ‘Foyil paper’ mai yawa yadda za ta dauki kazar sai ki zuba a ciki ki rufe ta gaba daya ba’a so kofa ko kadan saboda kada ruwa ya shiga sannan ki kara waro wata ki sake rurrufewa sosai.

Idan kuma kina da Steamer pot sai zuba ruwa a cikin ki dora akan steamer ki rufe ki dora a wuta ya yi kamar awa biyu za ki ga ya dahu.

Idan kuma baki da steamer za ki iya yi da tukunya da kwando, ki zuba ruwa a tukunya ki sa Kazar a kwando sai ki dora a tukunya ki dora a wuta kamar za ki yi dambo. A ci dadi lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda zaɓen cike gurbi ke gudana a sassan Najeriya

Ga hotunan yadda ake gudanar da zaɓen cike gurbi a sassan Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin ruwa ya nutse da mutum 30 a Sakkwato
  • AMA Foundation Da FGC Kaduna Sun Hada Kai Domin Tallafawa Ilimin Marayu A Jihar Kaduna 
  • Iran Ta Bada Agajin Gaggawa Ga Pakistan Bayan Ambaliyar Ruwa
  • Qalibof: Dole Ne Musulmi Su Hada kai Don Matsin Lamba Ga HKI
  • HOTUNA: Yadda zaɓen cike gurbi ke gudana a sassan Najeriya
  • Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli
  • Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah
  • NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa