Leadership News Hausa:
2025-10-15@06:07:02 GMT

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Published: 18th, May 2025 GMT

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Za ki samu kaza sai ki wanke ta, sannan ki tabbatar kin tsane mata ruwa ba’a barinta da ruwa ko kadan, sai ki zuba magi da gishiri da kori da kayan yaji da tafarnuwa idan kin so za ki dakata ko ki zuba ta haka, sai ki cakuda sosai ya shisshiga cikin kazar, sannan ki kawo albasa ki zuba wanda dama kin yankata a kwance ko a tsaye ba kanana ba saboda katta narke.

Sai ki kawo jajjagen tattasanki ki zuba, sai ki sake gaurayawa sosai, sannan ki ware ‘Foyil paper’ mai yawa yadda za ta dauki kazar sai ki zuba a ciki ki rufe ta gaba daya ba’a so kofa ko kadan saboda kada ruwa ya shiga sannan ki kara waro wata ki sake rurrufewa sosai.

Idan kuma kina da Steamer pot sai zuba ruwa a cikin ki dora akan steamer ki rufe ki dora a wuta ya yi kamar awa biyu za ki ga ya dahu.

Idan kuma baki da steamer za ki iya yi da tukunya da kwando, ki zuba ruwa a tukunya ki sa Kazar a kwando sai ki dora a tukunya ki dora a wuta kamar za ki yi dambo. A ci dadi lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta gayyaci CBN da bankunan kasuwanci kan yawan cire wa kwastomomi kuɗaɗe

Majalisar Wakilai ta ƙaddamar da bincike kan ƙaruwar koke-koken ’yan Najeriya kan yawan cire musu kuɗaɗe ba tare da bayani ba daga asusun ajiyarsu da bankunan kasuwanci ke yi.

Wannan mataki ya biyo bayan amincewa da wani ƙuduri da ɗan majalisa Hon. Tolani Shagaya (APC, Kwara) ya gabatar, inda ya nuna damuwa kan abin da ya kira “cire kuɗaɗe ba tare da bayani ba, da kuma yawan kuɗaɗen da ake karɓa ba bisa ka’ida ba,” duk da dokokin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya kafa.

An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna Kofin Duniya: Da sauran rina a kaba duk da Najeriya ta ci Jamhuriyar Benin 4-0

Yayin gabatar da ƙudurin a zaman majalisa ranar Talata, Shagaya ya ce duk da cewa ana sa ran bankuna su bayar da muhimman ayyukan kuɗi cikin farashi mai sauƙi, yawancin ’yan Najeriya na fuskantar cire kuɗaɗe da dama.

Ya ce cire kudade kamar kuɗin saƙon SMS, kuɗin gyaran kati, kuɗin kula da asusu, kuɗin canja wuri tsakanin bankuna, harajin tambari, da wasu cire-cire da ba a bayyana ba, da dama daga cikinsu ma ana maimaita su ko ba a bayyana su yadda ya kamata ba.

Ya nuna damuwa cewa irin waɗannan halaye na ci gaba da faruwa duk da cewa CBN ya fitar da ƙa’idoji masu bayyani kan yadda za a sarrafa kuɗaɗen da bankuna ke karɓa, amma yawancin bankuna na take waɗannan ƙa’idoji ba tare da jin tsoron hukunci ba.

“Irin waɗannan halaye na zalunci ya fi shafar ’yan kasuwa, masu ƙaramin karfi, ɗalibai, da ƙungiyoyin da ke cikin mawuyacin hali na tattalin arziki.

“Idan ba a gaggauta bincike da ɗaukar mataki ba, za su ci gaba da rage amincewar jama’a ga tsarin banki, su ƙara yawan waɗanda ba su da damar shiga harkokin kuɗi, kuma su lalata manufofin CBN na faɗaɗa damar shiga tsarin kuɗi,” in ji shi.

Bayan amincewa da ƙudurin, Majalisar ta bukaci CBN da ya fitar da jerin kuɗaɗen da aka amince da su cikin sauƙi ta yadda kowa zai fahimta, tare da tabbatar da aiwatar da hukunci ga bankunan da suka karya doka.

’Yan majalisar sun kuma bukaci babban bankin ƙasa da ya kafa wata hanya mai sauƙi da inganci don karɓar koke-koke daga abokan ciniki da suka fuskanci cire kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba ko fiye da kima.

Bugu da ƙari, Majalisar ta bukaci Hukumar Kare Masu Sayen Kaya (FCCPC) da sauran hukumomin da suka dace da su fara yaɗa shirye-shiryen wayar da kan jama’a a faɗin ƙasa don sanar da su haƙƙinsu dangane da kuɗaɗen da bankuna ke karɓa.

Ƙudurin ya kuma umarci Kwamitin Majalisa kan Dokokin Banki da Harkokin Bankuna da su gayyaci CBN da manyan bankunan kasuwanci don bayyana dalilan da ke sa ake ci gaba da cire kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba.

An umurci kwamitocin da su dawo da rahoto ga Majalisar cikin makonni huɗu domin ɗaukar matakin da ya dace na gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Majalisa ta gayyaci CBN da bankunan kasuwanci kan yawan cire wa kwastomomi kuɗaɗe
  • DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?
  • Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
  • Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
  • Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata
  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Yadda Ake Gurasa Ta Semovita