Leadership News Hausa:
2025-05-18@22:05:34 GMT

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Published: 18th, May 2025 GMT

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Za ki samu kaza sai ki wanke ta, sannan ki tabbatar kin tsane mata ruwa ba’a barinta da ruwa ko kadan, sai ki zuba magi da gishiri da kori da kayan yaji da tafarnuwa idan kin so za ki dakata ko ki zuba ta haka, sai ki cakuda sosai ya shisshiga cikin kazar, sannan ki kawo albasa ki zuba wanda dama kin yankata a kwance ko a tsaye ba kanana ba saboda katta narke.

Sai ki kawo jajjagen tattasanki ki zuba, sai ki sake gaurayawa sosai, sannan ki ware ‘Foyil paper’ mai yawa yadda za ta dauki kazar sai ki zuba a ciki ki rufe ta gaba daya ba’a so kofa ko kadan saboda kada ruwa ya shiga sannan ki kara waro wata ki sake rurrufewa sosai.

Idan kuma kina da Steamer pot sai zuba ruwa a cikin ki dora akan steamer ki rufe ki dora a wuta ya yi kamar awa biyu za ki ga ya dahu.

Idan kuma baki da steamer za ki iya yi da tukunya da kwando, ki zuba ruwa a tukunya ki sa Kazar a kwando sai ki dora a tukunya ki dora a wuta kamar za ki yi dambo. A ci dadi lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko

A taron kasashen larabawa karo na 34Th wanda ake gudanarwa a birnin Bagdaza na kasar Iraki, shuwagabannin kasashen larabawa sun bukaci tsagaita wuta a gaza sannan sun yi kira da aka kafa kasar Falasdinu mai zaman kanta.

Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa, shuwagabannin sun bukaci a magance matsalolin da suke faruwa a Siriya Lebanon da kuma sudan. Ana taron shuwagabannin kasashen larabwa a Bagdaza ne a dai dai lokacinda gwamnatin HKI take kara fadada hare-hare a kan zirin Gaza da kuma kashe Falasdinawa maza da mata da yara mutkar abinda zata iya kashewa.

Majiyar kiwon lafiya ta Gaza ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu sojojin HKI sun kashe falasdinawa kimani 53,272 mafi yawansu mata da yara, sannan wasu 120,673 kuma sun ji rauni . Ma’aikatar ta kara da cewa tun watan Marisa bayan da HKI ta sake komawa yaki a gaza ta kashe Falasdinawa 3131 sannan wasu 8,632 suka ji rauni.

A cikin bakin da suka sami halattar taron shuwagabannin kasashen larabawa karo na 34Th akwai babban sakataren MDD Antonio Gotteress kan cewa ana bukatar tsagaita wuta a gaza da gaggawa.  Sai kuma Firai ministan kasar Espaniya Pedro Sanchez ya bukaci a takurawa HKI ta dakatar kisan kiyashi a gaza.

Shuwagabannin sun ki amincewa da duk wani shiri na fidda Falasdinawa a gaza ko kuma kasarsu, kamar yadda Trump ya fada a farkon wannan shekarar.

Har’ila yau firai ministan kasar Iraki Muhammad shi’a Assudani, ya ware dalar Amurka miliyon $20 don sake gina Gaza sannan wasu miliyon 20 don sake gina kasar Lebanon. Ministan harkokin wajen kasar Siriya ne ya wakilci kasar a taron na Bagdaza saboda matsin lambar da wasu yan siyasa a kasar Iraki suka yiwa firai ministan kasar kan kada ya bar Ahmes Sharaa ya taka kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • ‘Yan Kasuwa 27 Sun Rasu A Wani Hatsarin Kwale-kwale A Kwara
  • Hukumar KNARDA Ta Ƙudiri Aniyar Yashe Madatsun Ruwa A Kano 
  • Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa
  • Jami’ar FUDAMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
  • Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko
  • Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba
  • Saudiya Ta Samar Da Wata Manhaja Ta Kiwon Lafiyar Mahajjata A Cikin Harsun 8 A Duniya